< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Elihou, poursuivant, dit:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Accorde-moi un peu d’attention, et je t’instruirai; car il reste encore des arguments en faveur de Dieu.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Je tirerai ma science de loin, et j’établirai l’équité de mon Dieu.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Car certes, mes paroles ne sont pas mensongères: c’est quelqu’un aux connaissances sûres qui est devant toi.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Vois, Dieu est puissant et il ignore le dédain; il est souverain par la force de la raison.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Il ne laisse point vivre le méchant, mais il fait triompher le bon droit des pauvres.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
Il ne détourne pas les yeux des justes, qu’il met de pair avec les rois sur le trône: il les installe solidement et les fait grandir.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Que s’ils sont enchaînés dans les fers, pris dans les liens de la misère,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
et qu’après leur avoir représenté leurs actes et leurs péchés, fruits de l’orgueil,
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
il ouvre leur oreille à la réprimande et les exhorte à revenir de l’iniquité,
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
s’ils écoutent et se soumettent, ils achèveront leurs jours dans le bonheur et leurs années dans les délices.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Mais s’ils n’écoutent point, ils finiront pas l’épée et périront faute d’intelligence.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Pervers de cœur, ils manifestent de la colère, refusent d’implorer Dieu quand il les charge de chaînes.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Aussi leur âme périt-elle en pleine jeunesse, leur vie s’éteint comme celle des infâmes libertins.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Mais le malheureux, il le sauve par sa misère même, et par la souffrance il ouvre son oreille aux conseils.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Aussi bien, il te fera passer de l’étreinte de l’adversité en un lieu spacieux, où n’existe nulle gène, et ta table sera couverte de mets succulents.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Si tu as subi pleinement le châtiment du méchant, c’est que châtiment et justice sont une force.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Crains donc que le dépit ne t’attire de nouveaux coups; ne te laisse pas égarer par la grandeur de la rançon.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Dieu peut-il priser assez tes cris suppliants pour t’épargner souffrances et durs efforts?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
N’Aspire point à la nuit, où les peuples sont enlevés de leur place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Garde-toi de te laisser aller au mal, car tu sembles le préférer à la souffrance.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Vois, Dieu est sublime dans sa force: existe-t-il un guide comme lui?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Qui lui dicte la voie qu’il doit suivre? Qui lui dira: "Tu commets des injustices?"
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Prends à cœur d’exalter son œuvre, que les humains célèbrent par leurs chants.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Les hommes l’admirent, le mortel la contemple de loin.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Oui, Dieu est grand: nous ne pouvons le comprendre; le nombre de ses années est incalculable.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Il attire les gouttes d’eau qui, à la suite de son brouillard, se résolvent en pluie.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Les nuages en ruissellent et s’épandent sur la foule des humains.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Sait-on seulement comprendre le déploiement des nuées, le fracas de son pavillon?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Vois, il s’enveloppe de sa lumière et il en couvre les profondeurs de cet océan de nuages.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Car il se sert d’eux pour juger les peuples ou leur donner de la nourriture en abondance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Il recouvre ses mains de flammes, qu’il dirige contre les rebelles.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Il révèle sa présence par son tonnerre, Instrument de colère contre les présomptueux.

< Ayuba 36 >