< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
厄里烏又接著說:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
你說過:「我在天主前是正義的。」你想這話合理嗎﹖
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
你還說過:「這與你何干﹖我若犯罪,我對你做了什麼﹖」
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
我今答覆你,以及和你在一起的友人。
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
請你仰視上天,且要靜觀,細看高於你的蒼天。
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
你若犯罪,為他有什麼害處﹖你若作惡多端,又能加害他什麼﹖
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
如果你為人正義,為他又有何益﹖或者他由你手中獲得什麼﹖
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
你的惡行只能加害與你類似的人,你的正義也只能有益於世人。
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
人因受暴虐過甚,必要哀號;因受強權的壓迫,必要呼籲。
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
但是沒有人說:「那造成我們,使人夜間歡唱,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
使我們比地上的走獸更聰明,使我們比天上的飛鳥更有智慧的天主在那裏﹖」
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
他們雖呼喊,天主卻不答應,這是因為惡人傲慢的原故。
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
他們空喊亂叫,天主決不俯聽,全能者決不垂視。
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
何況你說過:「你看不見他;但你的案件已放在他面前,你應等待他!」
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
你還說過:「他沒有發怒施罰,似乎不很理會罪過。」
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
的確,約伯開口盡說空話;由於無知,說了許多妄言。

< Ayuba 35 >