< Ayuba 34 >
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Escuchen, oh sabios, mis palabras, y ustedes, los que saben, escúchenme.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Porque el oído distingue las palabras y el paladar prueba el alimento.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Escojamos lo que es recto y sepamos entre nosotros lo que es bueno.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Porque Job dijo: Yo soy justo. ʼEL me quitó mi derecho.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
¿Debo mentir con respecto a mi derecho? Aunque no cometí transgresión, mi herida es incurable.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
¿Quién hay como Job, quien bebe el desprecio como agua,
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
quien se va en compañía con los transgresores y camina con los perversos?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Pues afirma: De nada le sirve al hombre deleitarse en ʼElohim.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Por tanto, hombres cuerdos, escúchenme: ¡Lejos esté de ʼElohim la perversidad, y de ʼEL-Shadday la injusticia!
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Porque Él paga al hombre según sus obras y hace que cada uno halle según su camino.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Ciertamente ʼElohim no obra perversamente, ni ʼEL-Shadday pervierte la justicia.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
¿Quién le dio autoridad sobre la tierra? ¿Quién le confió todo el universo?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Si Él determina hacer así, retirar para Sí mismo su Espíritu y su aliento,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
toda carne perecería juntamente, y el hombre volvería al polvo.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Si tienes entendimiento, escucha esto, escucha el sonido de mis palabras:
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
¿Gobernará el que aborrece la justicia? ¿Te atreves a condenar al Justo poderoso,
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
a Aquél que declara a un rey inútil y perversos a los nobles,
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Quien no muestra parcialidad con príncipes, ni considera al rico por encima del pobre? Porque todos ellos son la obra de sus manos.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
De repente a medianoche mueren, las gentes se estremecen y ya no están. Los poderosos son derribados y no por mano.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Porque los ojos de Él están sobre las sendas del hombre y observan todos sus pasos.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
No hay oscuridad ni sombras donde puedan ocultarse los que hacen iniquidad.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Pues no le impone plazo al hombre, para que comparezca a juicio ante ʼEL.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Él quebranta a los poderosos sin indagar y pone a otros en lugar de ellos.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Por cuanto conoce las obras de ellos, los trastorna en una noche, y quedan deshechos.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Los azota por sus perversidades en un lugar público,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
porque se apartaron de seguirlo. No consideraron alguno de los caminos de Él.
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Buscaron que el clamor del pobre llegara a Él, y que escuchara el clamor de los afligidos.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Cuando Él da tranquilidad, ¿quién entonces lo inculpará? Si esconde su rostro, ¿quién lo mirará? Esto ocurre tanto con respecto a una nación como con respecto a un hombre,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
para evitar que reine el impío e imponga trampas al pueblo.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Porque, ¿alguno le dijo a ʼEL: Generé mi castigo, no pecaré más,
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
enséñame Tú lo que yo no veo? ¡Si obré mal, no lo haré más!
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
¿Retribuirá según tus condiciones, porque tú rechazas las de Él? Si rechazas o si aceptas, Él te retribuirá, no yo. Y si no es así, dí lo que sabes.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Los hombres de entendimiento me lo dirán, y el hombre sabio que me escucha:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Que Job no habló con sabiduría, que sus palabras fueron sin discernimiento,
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
que Job debe ser probado hasta el límite, porque respondió como los perversos,
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
y a su pecado añade rebelión. Bate palmas ante nosotros y multiplica sus palabras contra ʼEL.