< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
“Lakini Ayubu, sasa, sikiliza maneno yangu; zingatia kila kitu nitakachosema.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Karibu nitafungua kinywa changu; maneno yangu yapo katika ncha ya ulimi wangu.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Maneno yangu yanatoka katika moyo mnyofu; midomo yangu hunena kwa uaminifu yale niyajuayo.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
Roho wa Mungu ameniumba; pumzi ya Mwenyezi hunipa uhai.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Unijibu basi, kama unaweza; jiandae kunikabili mimi.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Mimi ni kama wewe mbele za Mungu; mimi pia nimetolewa kwenye udongo.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Huna sababu ya kuniogopa, wala mkono wangu haupaswi kukulemea.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
“Lakini umesema nikiwa ninakusikia, nami nilisikia maneno yenyewe:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
‘Mimi ni safi na sina dhambi; mimi ni safi na sina hatia.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Lakini bado Mungu amepata dosari kwangu, naye ananiona kama adui yake.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Ananifunga miguu kwa pingu, tena anaziangalia njia zangu zote kwa karibu.’
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
“Lakini mimi ninakuambia, katika jambo hili wewe una makosa, kwa maana Mungu ni mkuu kuliko mwanadamu.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Kwa nini unamlalamikia kwamba yeye hamjibu mwanadamu?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Kwa kuwa Mungu husema, wakati huu kwa njia moja, au wakati mwingine kwa njia nyingine, ingawa mwanadamu anaweza asielewe.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
Mungu husema na mwanadamu katika ndoto, katika maono ya usiku, wakati usingizi mzito uwaangukiapo wanadamu wasinziapo vitandani mwao,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
anaweza akasemea masikioni mwao, na kuwatia hofu kwa maonyo,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
ili kumgeuza mtu kutoka kwenye kutenda mabaya na kumwepusha na kiburi,
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
kuiokoa nafsi yake na shimo, uhai wake usiangamizwe kwa upanga.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
Mtu anaweza kutiwa adabu kwa maumivu kitandani mwake, kwa dhiki za mfululizo katika mifupa yake,
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
kiasi kwamba maisha yake yenyewe yanakataa chakula nayo nafsi yake ikakichukia kabisa hata chakula kizuri.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Nyama ya mwili wake huisha kwa kukonda, nayo mifupa yake ambayo mwanzoni ilikuwa imefichika, sasa inatokeza nje.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Nafsi yake inakaribia kaburi, nao uhai wake karibu na wajumbe wa kifo.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
“Kama bado kuna malaika upande wake kama mtetezi, mmoja miongoni mwa elfu, wa kumwambia mwanadamu lililo jema kwake,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
kumwonea huruma na kusema, ‘Mwokoe asije akatumbukia shimoni; nimepata ukombozi kwa ajili yake’:
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
ndipo nyama ya mwili wake hufanywa mpya kama ya mtoto; hurudishwa upya kama siku za ujana wake.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Humwomba Mungu, akapata kibali kwake, huuona uso wa Mungu na kushangilia kwa furaha; Mungu humrudisha katika hali yake ya uadilifu.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Ndipo huja mbele za watu na kusema, ‘Nilitenda dhambi na kupotosha kilichokuwa haki, lakini sikuadhibiwa kama nilivyostahili.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Alinikomboa nafsi yangu nisitumbukie shimoni, nami nitaishi ili kuufurahia mwanga.’
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
“Mungu hufanya haya yote kwa mwanadamu; mara mbili hata mara tatu,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
ili aigeuze nafsi yake toka shimoni, ili nuru ya uzima imwangazie.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
“Ayubu, zingatia, nisikilize mimi; nyamaza, nami nitanena.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Kama unalo lolote la kusema, unijibu; sema, kwa maana ninataka uonekane huna hatia.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Lakini kama huna la kusema, basi nisikilize mimi; nyamaza, nami nitakufundisha hekima.”

< Ayuba 33 >