< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
[Audi igitur, Job, eloquia mea, et omnes sermones meos ausculta.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Ecce aperui os meum: loquatur lingua mea in faucibus meis.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Simplici corde meo sermones mei, et sententiam puram labia mea loquentur.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
Spiritus Dei fecit me, et spiraculum Omnipotentis vivificavit me.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Si potes, responde mihi, et adversus faciem meam consiste.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Ecce, et me sicut et te fecit Deus, et de eodem luto ego quoque formatus sum.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Verumtamen miraculum meum non te terreat, et eloquentia mea non sit tibi gravis.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Dixisti ergo in auribus meis, et vocem verborum tuorum audivi:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
Mundus sum ego, et absque delicto: immaculatus, et non est iniquitas in me.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Quia querelas in me reperit, ideo arbitratus est me inimicum sibi.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Posuit in nervo pedes meos; custodivit omnes semitas meas.
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Hoc est ergo in quo non es justificatus: respondebo tibi, quia major sit Deus homine.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Adversus eum contendis, quod non ad omnia verba responderit tibi?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Semel loquitur Deus, et secundo idipsum non repetit.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
Per somnium, in visione nocturna, quando irruit sopor super homines, et dormiunt in lectulo,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
tunc aperit aures virorum, et erudiens eos instruit disciplina,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
ut avertat hominem ab his quæ facit, et liberet eum de superbia,
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
eruens animam ejus a corruptione, et vitam illius ut non transeat in gladium.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
Increpat quoque per dolorem in lectulo, et omnia ossa ejus marcescere facit.
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
Abominabilis ei fit in vita sua panis, et animæ illius cibus ante desiderabilis.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Tabescet caro ejus, et ossa, quæ tecta fuerant, nudabuntur.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Appropinquavit corruptioni anima ejus, et vita illius mortiferis.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Si fuerit pro eo angelus loquens, unus de millibus, ut annuntiet hominis æquitatem,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
miserebitur ejus, et dicet: Libera eum, ut non descendat in corruptionem: inveni in quo ei propitier.
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
Consumpta est caro ejus a suppliciis: revertatur ad dies adolescentiæ suæ.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Deprecabitur Deum, et placabilis ei erit: et videbit faciem ejus in jubilo, et reddet homini justitiam suam.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Respiciet homines, et dicet: Peccavi, et vere deliqui, et ut eram dignus, non recepi.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Liberavit animam suam, ne pergeret in interitum, sed vivens lucem videret.
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Ecce hæc omnia operatur Deus tribus vicibus per singulos,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
ut revocet animas eorum a corruptione, et illuminet luce viventium.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Attende, Job, et audi me: et tace, dum ego loquor.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Si autem habes quod loquaris, responde mihi: loquere, volo enim te apparere justum.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Quod si non habes, audi me: tace, et docebo te sapientiam.]

< Ayuba 33 >