< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Wherefore, Job, I pray you, hear my speeches, and hearken to all my words.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Behold, now I have opened my mouth, my tongue has spoken in my mouth.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
My words shall be of the uprightness of my heart: and my lips shall utter knowledge clearly.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
The spirit of God has made me, and the breath of the Almighty has given me life.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
If you can answer me, set your words in order before me, stand up.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Behold, I am according to your wish in God's position: I also am formed out of the clay.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Behold, my terror shall not make you afraid, neither shall my hand be heavy upon you.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Surely you have spoken in mine hearing, and I have heard the voice of your words, saying,
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
I am clean without transgression, I am innocent; neither is there iniquity in me.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Behold, he finds occasions against me, he counts me for his enemy,
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
He puts my feet in the stocks, he marks all my paths.
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Behold, in this you are not just: I will answer you, that God is greater than man.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Why do you strive against him? for he gives not account of any of his matters.
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
For God speaks once, yea twice, yet man perceives it not.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
In a dream, in a vision of the night, when deep sleep falls upon men, in slumberings upon the bed;
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
Then he opens the ears of men, and seals their instruction,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
That he may withdraw man from his purpose, and hide pride from man.
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
He keeps back his soul from the pit, and his life from perishing by the sword.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
He is chastened also with pain upon his bed, and the multitude of his bones with strong pain:
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
So that his life detests bread, and his soul dainty food.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
His flesh is consumed away, that it cannot be seen; and his bones that were not seen stick out.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Yea, his soul draws near unto the grave, and his life to the destroyers.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
If there be a messenger with him, an interpreter, one among a thousand, to show unto man his uprightness:
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
Then he is gracious unto him, and says, Deliver him from going down to the pit: I have found a ransom.
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
His flesh shall be fresher than a child's: he shall return to the days of his youth:
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
He shall pray unto God, and he will be favourable unto him: and he shall see his face with joy: for he will render unto man his righteousness.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
He looks upon men, and if any say, I have sinned, and perverted that which was right, and it profited me not;
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
He will deliver his soul from going into the pit, and his life shall see the light.
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Lo, all these things works God oftentimes with man,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
To bring back his soul from the pit, to be enlightened with the light of the living.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Mark well, O Job, hearken unto me: hold your peace, and I will speak.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
If you have anything to say, answer me: speak, for I desire to justify you.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
If not, hearken unto me: hold your peace, and I shall teach you wisdom.

< Ayuba 33 >