< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
“I made a covenant for my eyes, And how do I attend to a virgin?
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
And what [is] the portion of God from above? And the inheritance of the Mighty from the heights?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Is not calamity to the perverse? And strangeness to workers of iniquity?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Does He not see my ways, And number all my steps?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
If I have walked with vanity, And my foot hurries to deceit,
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
He weighs me in righteous balances, And God knows my integrity.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
If my step turns aside from the way, And my heart has gone after my eyes, And blemish has cleaved to my hands,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
Let me sow—and another eat, And let my products be rooted out.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
If my heart has been enticed by a woman, And I laid wait by the opening of my neighbor,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
Let my wife grind to another, And let others bend over her.
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
For it [is] a wicked thing, and a judicial iniquity;
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
For it [is] a fire, it consumes to destruction, And takes root among all my increase,
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
If I despise the cause of my manservant, And of my handmaid, In their contending with me,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
Then what do I do when God arises? And when He inspects, What do I answer Him?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Did He that made me in the womb not make him? Indeed, One prepares us in the womb.
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
If I withhold the poor from pleasure, And consume the eyes of the widow,
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
And I eat my morsel by myself, And the orphan has nothing [to] eat of it,
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
(But from my youth He grew up with me as [with] a father, And from the belly of my mother I am led),
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
If I see [any] perishing without clothing, And there is no covering for the needy,
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
If his loins have not blessed me, And from the fleece of my sheep He does not warm himself,
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
If I have waved my hand at the fatherless, When I see [him] in the gate of my court,
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
Let my shoulder fall from its blade, And the bone from my arm be broken.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
For calamity [from] God [is] a dread to me, And because of His excellence I am not able.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
If I have made gold my confidence, And to the pure gold have said, My trust;
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
If I rejoice because my wealth [is] great, And because my hand has found abundance,
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
If I see the light when it shines, And the precious moon walking,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
And my heart is enticed in secret, And my hand kisses my mouth,
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
It also [is] a judicial iniquity, For I had lied to God above.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
If I rejoice at the ruin of my hater, And stirred up myself when evil found him,
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
Indeed, I have not permitted my mouth to sin, To ask with an oath his life.
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
If not, say, O men of my tent: O that we had of his flesh, we are not satisfied.
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
A stranger does not lodge in the street, I open my doors to the traveler.
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
If I have covered my transgressions as Adam, To hide my iniquity in my bosom,
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
Because I fear a great multitude, And the contempt of families frightens me, Then I am silent, I do not go out of the opening.
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Who gives to me a hearing? Behold, my mark. The Mighty One answers me, And my adversary has written a bill.
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
If not—on my shoulder I take it up, I bind it [as] a crown on myself.
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
The number of my steps I tell Him, As a leader I approach Him.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
If my land cries out against me, And together its furrows weep,
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
If I consumed its strength without money, And the life of its possessors, I have caused to breathe out,
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
Instead of wheat let a thorn go forth, And instead of barley a useless weed!” The words of Job are finished.

< Ayuba 31 >