< Ayuba 3 >
1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
After this Job began speaking, cursing the day of his birth.
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
“Wipe out the day I was born, and the night when it was announced that a boy had been conceived.
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Turn that day to darkness. God above should not remember it. Don't let light shine on it.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Take it back, darkness and death-shadow. A black cloud should overshadow it. It should be as terrifying as the darkness of an eclipse during the day.
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Blot out that night as if it never existed. Don't count it on the calendar. Don't let it have a day in any month.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Let that night be childless, with no sounds of happiness heard.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Those who place curses on certain days should curse it, those who have the power to raise Leviathan.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Its early morning stars should stay dark. Looking for light, may none come, may it not see the glimmer of dawn
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
for it did not shut my mother's womb to prevent me from seeing trouble.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Why wasn't I stillborn? Why didn't I die at birth?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Why was there a lap for me to lie on, or breasts for me to suck?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
For now I would be lying down in peace. I would be sleeping and at rest,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
along with the kings of this world and their officials whose palaces now lie in ruins,
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
or with noblemen who collected gold and filled their houses with silver.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Why wasn't I a miscarriage, buried in secret, a baby who never saw the light?
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
There in the grave the wicked give no more trouble, and those whose strength is gone have their rest.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
There prisoners take it easy—they don't hear the commands of their oppressors.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Both small and great are there, and slaves are freed from their masters.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Why does God give life to those who are suffering, living bitterly miserable lives,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
those who are waiting for death that does not come and who are looking for death more desperately than hunting for treasure?
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
They're so incredibly happy when the reach the grave!
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
Why is light given to someone who doesn't know where they're going, someone God has fenced in?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
My groans are the bread I eat; my raging tears are the water I drink.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
For all that I feared has happened to me; everything that I dreaded has come upon me.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
I have no peace, no quiet, no rest. All that comes is rage.”