< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Eyüp yine anlatmaya başladı:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
“Keşke geçen aylar geri gelseydi, Tanrı'nın beni kolladığı,
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
Kandilinin başımın üstünde parladığı, Işığıyla karanlıkta yürüdüğüm günler,
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
Keşke olgunluk günlerim geri gelseydi, Tanrı'nın çadırımı dostça koruduğu,
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
Her Şeye Gücü Yeten'in henüz benimle olduğu, Çocuklarımın çevremde bulunduğu,
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
Yollarımın sütle yıkandığı, Yanımdaki kayanın zeytinyağı akıttığı günler!
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
“Kent kapısına gidip Kürsümü meydana koyduğumda,
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
Gençler beni görüp gizlenir, Yaşlılar kalkıp ayakta dururlardı;
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Önderler konuşmaktan çekinir, Elleriyle ağızlarını kaparlardı;
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
Soyluların sesi kesilir, Dilleri damaklarına yapışırdı.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
Beni duyan kutlar, Beni gören överdi;
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Çünkü yardım isteyen yoksulu, Desteği olmayan öksüzü kurtarırdım.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
Ölmekte olanın hayır duasını alır, Dul kadının yüreğini sevinçten coştururdum.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Doğruluğu giysi gibi giyindim, Adalet kaftanım ve sarığımdı sanki.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
Körlere göz, Topallara ayaktım.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
Yoksullara babalık eder, Garibin davasını üstlenirdim.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Haksızın çenesini kırar, Avını dişlerinin arasından kapardım.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
“‘Son soluğumu yuvamda vereceğim’ diye düşünüyordum, ‘Günlerim kum taneleri kadar çok.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
Köküm sulara erişecek, Çiy geceyi dallarımda geçirecek.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
Aldığım övgüler tazelenecek, Elimdeki yay yenilenecek.’
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
“İnsanlar beni saygıyla dinler, Öğüdümü sessizce beklerlerdi.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Ben konuştuktan sonra onlar konuşmazdı, Sözlerim üzerlerine damlardı.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Yağmuru beklercesine beni bekler, Son yağmurları içercesine sözlerimi içerlerdi.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Kendilerine gülümsediğimde gözlerine inanmazlardı, Güler yüzlülüğüm onlara cesaret verirdi.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Onların yolunu ben seçer, başlarında dururdum, Askerlerinin ortasında kral gibi otururdum, Yaslıları avutan biri gibiydim.

< Ayuba 29 >