< Ayuba 29 >
1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
addidit quoque Iob adsumens parabolam suam et dixit
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
quis mihi tribuat ut sim iuxta menses pristinos secundum dies quibus Deus custodiebat me
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
quando splendebat lucerna eius super caput meum et ad lumen eius ambulabam in tenebris
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
sicut fui in diebus adulescentiae meae quando secreto Deus erat in tabernaculo meo
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
quando erat Omnipotens mecum et in circuitu meo pueri mei
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
quando lavabam pedes meos butyro et petra fundebat mihi rivos olei
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
quando procedebam ad portam civitatis et in platea parabant cathedram mihi
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
videbant me iuvenes et abscondebantur et senes adsurgentes stabant
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
principes cessabant loqui et digitum superponebant ori suo
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
vocem suam cohibebant duces et lingua eorum gutturi suo adherebat
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
auris audiens beatificabat me et oculus videns testimonium reddebat mihi
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
quod liberassem pauperem vociferantem et pupillum cui non esset adiutor
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
benedictio perituri super me veniebat et cor viduae consolatus sum
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
iustitia indutus sum et vestivit me sicut vestimento et diademate iudicio meo
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
oculus fui caeco et pes claudo
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
pater eram pauperum et causam quam nesciebam diligentissime investigabam
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
conterebam molas iniqui et de dentibus illius auferebam praedam
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
dicebamque in nidulo meo moriar et sicut palma multiplicabo dies
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
radix mea aperta est secus aquas et ros morabitur in messione mea
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
gloria mea semper innovabitur et arcus meus in manu mea instaurabitur
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
qui me audiebant expectabant sententiam et intenti tacebant ad consilium meum
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
verbis meis addere nihil audebant et super illos stillabat eloquium meum
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
expectabant me sicut pluviam et os suum aperiebant quasi ad imbrem serotinum
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
si quando ridebam ad eos non credebant et lux vultus mei non cadebat in terram
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
si voluissem ire ad eos sedebam primus cumque sederem quasi rex circumstante exercitu eram tamen maerentium consolator