< Ayuba 25 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then Bildad the Shuhite replied:
2 “Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
“Dominion and awe belong to God; He establishes harmony in the heights of heaven.
3 Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
Can His troops be numbered? On whom does His light not rise?
4 Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
How then can a man be just before God? How can one born of woman be pure?
5 In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
If even the moon does not shine, and the stars are not pure in His sight,
6 mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”
how much less man, who is but a maggot, and the son of man, who is but a worm!”

< Ayuba 25 >