< Ayuba 24 >

1 “Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
Howe should not the times be hid from the Almightie, seeing that they which knowe him, see not his dayes?
2 Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
Some remoue the land marks, that rob the flockes and feede thereof.
3 Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
They leade away the asse of the fatherles: and take the widowes oxe to pledge.
4 Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
They make the poore to turne out of the way, so that the poore of the earth hide themselues together.
5 Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
Behold, others as wilde asses in the wildernesse, goe forth to their businesse, and rise early for a praye: the wildernesse giueth him and his children foode.
6 Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
They reape his prouision in the fielde, but they gather the late vintage of the wicked.
7 Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
They cause the naked to lodge without garment, and without couering in the colde.
8 Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
They are wet with the showres of the moutaines, and they imbrace the rocke for want of a couering.
9 Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
They plucke the fatherles from the breast, and take the pledge of the poore.
10 Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
They cause him to go naked without clothing, and take the glening from the hungrie.
11 Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
They that make oyle betweene their walles, and treade their wine presses, suffer thirst.
12 Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
Men cry out of the citie, and the soules of the slayne cry out: yet God doth not charge them with follie.
13 “Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
These are they, that abhorre the light: they know not the wayes thereof, nor continue in the paths thereof.
14 Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
The murtherer riseth earely and killeth the poore and the needie: and in the night he is as a theefe.
15 Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
The eye also of the adulterer waiteth for the twilight, and sayth, None eye shall see me, and disguiseth his face.
16 Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
They digge through houses in the darke, which they marked for themselues in the daye: they knowe not the light.
17 Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
But the morning is euen to them as the shadow of death: if one knowe them, they are in the terrours of the shadowe of death.
18 “Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
He is swift vpon the waters: their portion shalbe cursed in the earth: he will not behold the way of the vineyardes.
19 Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol h7585)
As the dry ground and heate consume the snowe waters, so shall the graue the sinners. (Sheol h7585)
20 Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
The pitifull man shall forget him: the worme shall feele his sweetenes: he shalbe no more remembered, and the wicked shalbe broke like a tree.
21 Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
He doth euil intreat ye barren, that doeth not beare, neither doeth he good to the widowe.
22 Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
He draweth also the mighty by his power, and when he riseth vp, none is sure of life.
23 Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
Though men giue him assurance to be in safetie, yet his eyes are vpon their wayes.
24 Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
They are exalted for a litle, but they are gone, and are brought lowe as all others: they are destroyed, and cut off as the toppe of an eare of corne.
25 “In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”
But if it be not so, where is he? or who wil proue me a lyer, and make my words of no value?

< Ayuba 24 >