< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Mais, répondant, Job dit:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Maintenant encore mes paroles sont pleines d’amertume, et la violence de ma plaie s’est plus aggravée que mes gémissements.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Qui m’accordera que je sache trouver Dieu, et arriver jusqu’à son trône?
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
J’exposerai ma cause devant lui, et je remplirai ma bouche de récriminations,
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
Afin que je sache les paroles qu’il me répondra, et que je comprenne ce qu’il me dira.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Je ne veux pas qu’il lutte contre moi avec beaucoup de force, ni qu’il m’accable par le poids de sa grandeur.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Qu’il mette en avant contre moi l’équité, et ma cause obtiendra la victoire.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Si je vais à l’orient, il ne paraît pas; si à l’occident, je ne l’aperçois point.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Si c’est à gauche, que ferai-je? je ne l’atteindrai pas; si je me tourne à droite, je ne le verrai pas.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Mais pour lui, il connaît ma voie, et il m’a éprouvé comme l’or qui passe par le feu.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Mon pied a suivi ses traces; j’ai gardé sa voie, et je ne m’en suis pas détourné,
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
Je ne me suis pas écarté des commandements sortis de ses lèvres, et j’ai caché dans mon sein les paroles de sa bouche.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Car lui est seul Tout-Puissant, et personne ne peut détourner sa pensée; et tout ce que son âme a voulu, elle l’a fait.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Quand il aura accompli en moi sa volonté, il aura encore un grand nombre de moyens semblables à sa disposition.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Et c’est pour cela qu’à sa face je suis troublé, et que, le considérant, je suis agité par la crainte.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Dieu a amolli mon cœur, et, le Tout-Puissant m’a épouvanté.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Car je n’ai pas péri à cause des ténèbres qui me pressent, et une obscurité n’a pas couvert ma face.

< Ayuba 23 >