< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Bvt Iob answered and sayd,
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Though my talke be this day in bitternes, and my plague greater then my groning,
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Would God yet I knew how to finde him, I would enter vnto his place.
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
I would pleade the cause before him, and fill my mouth with arguments.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
I would knowe the wordes, that he would answere me, and would vnderstand what he would say vnto me.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Would he plead against me with his great power? No, but he would put strength in me.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
There the righteous might reason with him, so I shoulde be deliuered for euer from my Iudge.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Behold, if I go to the East, he is not there: if to the West, yet I can not perceiue him:
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
If to the North where he worketh, yet I cannot see him: he wil hide himselfe in the South, and I cannot beholde him.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
But he knoweth my way, and trieth mee, and I shall come forth like the gold.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
My foote hath followed his steps: his way haue I kept, and haue not declined.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
Neyther haue I departed from the commandement of his lippes, and I haue esteemed the words of his mouth more then mine appointed foode.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Yet he is in one minde, and who can turne him? yea, he doeth what his minde desireth.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
For he will performe that, which is decreed of me, and many such things are with him.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Therefore I am troubled at his presence, and in considering it, I am afraid of him.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
For God hath softened mine heart, and the Almightie hath troubled me.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
For I am not cut off in darknesse, but he hath hid the darkenesse from my face.

< Ayuba 23 >