< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Elifaz temanita habló otra vez:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
¿Puede el hombre dar provecho a ʼElohim? ¿Puede el hombre vigoroso serle útil?
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
¿ʼEL-Shadday tiene deleite en que tú seas justo? ¿Qué gana Él si tus caminos son rectos?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
¿Te reprocha o te lleva a juicio por tu reverencia a Él?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
¿No son grandes tus perversidades, y tus iniquidades no tienen fin?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Porque sin razón tomaste prendas a tus hermanos y al desnudo despojaste de sus ropas.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
No diste de beber al sediento y negaste el pan al hambriento.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
Pero la tierra pertenece al hombre poderoso, honorable que vive en ella.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Despediste a las viudas con las manos vacías, y los brazos de los huérfanos fueron quebrantados.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Por eso hay trampas alrededor de ti, te espantan terrores repentinos,
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
o hay oscuridad para que no veas, y te cubre la abundancia de aguas.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
¿No está ʼEloah en la altura del cielo? ¡Mira cuán elevadas están las estrellas!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Y dijiste: ¿Qué sabe ʼElohim? ¿Podrá distinguir a través de la oscuridad?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Las nubes son un lugar de escondite para Él, así que no puede ver. Él pasea por la bóveda celeste.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
¿Seguirás en la senda antigua que pisaron los hombres perversos,
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
los cuales fueron arrastrados antes de tiempo, cuyos cimientos fueron arrasados por un río?
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Ellos decían a ʼElohim: ¡Apártate de nosotros! ¿Qué puede hacernos ʼEL-Shadday?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Aunque Él llenó sus viviendas de bienes, lejos esté de mí el consejo de los perversos.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Los justos lo ven y se alegran. El inocente se burla de ellos:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
¡En verdad nuestros adversarios fueron destruidos, y lo que queda de ellos lo devora el fuego!
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Reconcíliate y tendrás paz con Él, y por ello te vendrá bien.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Acepta la instrucción de su boca, y guarda sus dichos en tu corazón.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Si te vuelves a ʼEL-Shadday, serás reedificado. Si alejas la iniquidad de tu casa,
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
y lanzas tu tesoro al polvo, y el oro de Ofir, como piedras del arroyo.
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
Entonces ʼEL-Shadday será tu oro y plata preciosa para ti.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Entonces te deleitarás en ʼEL-Shadday, y levantarás tu rostro hacia ʼElohim.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Orarás a Él, y te escuchará, y tú podrás pagar tus votos.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Cuando decidas una cosa, te será establecida y brillará la luz en tus caminos.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Cuando estés abatido, hablarás con confianza: ¡Y a la persona humilde Él salvará!
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Librará al inocente. Escapará a causa de la limpieza de tus manos.

< Ayuba 22 >