< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
And Eliphaz the Temanite answers and says:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
“Is a man profitable to God, Because a wise man is profitable to himself?
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Is it a delight to the Mighty One That you are righteous? Is it gain, That you make your ways perfect?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Because of your reverence Does He reason [with] you? He enters with you into judgment:
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Is your wickedness not abundant? And there is no end to your iniquities.
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
For you take a pledge of your brother for nothing, And you strip off the garments of the naked.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
You do not cause the weary to drink water, And you withhold bread from the hungry.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
As for the man of arm—he has the earth, And the accepted of face—he dwells in it.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
You have sent widows away empty, And the arms of the fatherless are bruised.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Therefore snares [are] all around you, And sudden fear troubles you.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Or darkness—you do not see, And abundance of waters covers you.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Is God not high [in] the heavens? And see the summit of the stars, That they are high.
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
And you have said, How has God known? Does He judge through thickness?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Thick clouds [are] a secret place to Him, And He does not see, And He habitually walks [above] the circle of the heavens.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Do you observe the path of the age, That men of iniquity have trodden,
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Who have been cut down unexpectedly? A flood is poured out on their foundation.
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Those saying to God, Turn aside from us, And what does the Mighty One do to them?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
And He has filled their houses [with] good (And the counsel of the wicked Has been far from me).
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
The righteous see and they rejoice, And the innocent mocks at them:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
Surely our substance has not been cut off, And fire has consumed their excellence.
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Now acquaint yourself with Him, and be at peace, Thereby your increase [is] good.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Please receive a law from His mouth, And set His sayings in your heart.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
If you return to the Mighty you are built up, You put iniquity far from your tents.
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
So as to set a defense on the dust, And a covering on a rock of the valleys.
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
And the Mighty has been your defense, And silver [is] strength to you.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
For then you delight yourself on the Mighty, And lift up your face to God,
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
You make supplication to Him, And He hears you, And you complete your vows.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
And you decree a saying, And it is established to you, And light has shone on your ways.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
For they have made low, And you say, Lift up. And He saves the bowed down of eyes.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
He delivers the one [who is] not innocent, Indeed, he has been delivered By the cleanness of your hands.”

< Ayuba 22 >