< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job answered:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
“Listen carefully to my words; let this be your consolation to me.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Bear with me while I speak; then, after I have spoken, you may go on mocking.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Is my complaint against a man? Then why should I not be impatient?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Look at me and be appalled; put your hand over your mouth.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
When I remember, terror takes hold, and my body trembles in horror.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Why do the wicked live on, growing old and increasing in power?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Their descendants are established around them, and their offspring before their eyes.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Their homes are safe from fear; no rod of punishment from God is upon them.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Their bulls breed without fail; their cows bear calves and do not miscarry.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
They send forth their little ones like a flock; their children skip about,
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
singing to the tambourine and lyre and making merry at the sound of the flute.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
They spend their days in prosperity and go down to Sheol in peace. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Yet they say to God: ‘Leave us alone! For we have no desire to know Your ways.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Who is the Almighty, that we should serve Him, and what would we gain if we pray to Him?’
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Still, their prosperity is not in their own hands, so I stay far from the counsel of the wicked.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
How often is the lamp of the wicked put out? Does disaster come upon them? Does God, in His anger, apportion destruction?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Are they like straw before the wind, like chaff swept away by a storm?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
It is said that God lays up one’s punishment for his children. Let God repay the man himself, so he will know it.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Let his eyes see his own destruction; let him drink for himself the wrath of the Almighty.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
For what does he care about his household after him, when the number of his months has run out?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Can anyone teach knowledge to God, since He judges those on high?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
One man dies full of vigor, completely secure and at ease.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
His body is well nourished, and his bones are rich with marrow.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Yet another man dies in the bitterness of his soul, having never tasted prosperity.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
But together they lie down in the dust, and worms cover them both.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Behold, I know your thoughts full well, the schemes by which you would wrong me.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
For you say, ‘Where now is the nobleman’s house, and where are the tents in which the wicked dwell?’
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Have you never asked those who travel the roads? Do you not accept their reports?
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
Indeed, the evil man is spared from the day of calamity, delivered from the day of wrath.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Who denounces his behavior to his face? Who repays him for what he has done?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
He is carried to the grave, and watch is kept over his tomb.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
The clods of the valley are sweet to him; everyone follows behind him, and those before him are without number.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
So how can you comfort me with empty words? For your answers remain full of falsehood.”

< Ayuba 21 >