< Ayuba 19 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
约伯回答说:
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
你们搅扰我的心, 用言语压碎我要到几时呢?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
你们这十次羞辱我; 你们苦待我也不以为耻。
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
果真我有错, 这错乃是在我。
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
你们果然要向我夸大, 以我的羞辱为证指责我,
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
就该知道是 神倾覆我, 用网罗围绕我。
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
我因委曲呼叫,却不蒙应允; 我呼求,却不得公断。
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
神用篱笆拦住我的道路,使我不得经过; 又使我的路径黑暗。
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
他剥去我的荣光, 摘去我头上的冠冕。
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
他在四围攻击我,我便归于死亡, 将我的指望如树拔出来。
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
他的忿怒向我发作, 以我为敌人。
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
他的军旅一齐上来, 修筑战路攻击我, 在我帐棚的四围安营。
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
他把我的弟兄隔在远处, 使我所认识的全然与我生疏。
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
我的亲戚与我断绝; 我的密友都忘记我。
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
在我家寄居的, 和我的使女都以我为外人; 我在他们眼中看为外邦人。
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
我呼唤仆人, 虽用口求他,他还是不回答。
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
我口的气味,我妻子厌恶; 我的恳求,我同胞也憎嫌。
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
连小孩子也藐视我; 我若起来,他们都嘲笑我。
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
我的密友都憎恶我; 我平日所爱的人向我翻脸。
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
我的皮肉紧贴骨头; 我只剩牙皮逃脱了。
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
我朋友啊,可怜我!可怜我! 因为 神的手攻击我。
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
你们为什么仿佛 神逼迫我, 吃我的肉还以为不足呢?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
惟愿我的言语现在写上, 都记录在书上;
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
用铁笔镌刻, 用铅灌在磐石上,直存到永远。
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
我知道我的救赎主活着, 末了必站立在地上。
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
我这皮肉灭绝之后, 我必在肉体之外得见 神。
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
我自己要见他, 亲眼要看他,并不像外人。 我的心肠在我里面消灭了!
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
你们若说:我们逼迫他要何等地重呢? 惹事的根乃在乎他;
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
你们就当惧怕刀剑; 因为忿怒惹动刀剑的刑罚, 使你们知道有报应。

< Ayuba 19 >