< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
And Bildad the Shuhite answers and says:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
“When do you set an end to words? Consider, and afterward we speak.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Why have we been reckoned as livestock? We have been defiled in your eyes!
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
He is tearing himself in his anger. Is earth forsaken for your sake? And is a rock removed from its place?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Also, the light of the wicked is extinguished. And there does not shine a spark of his fire.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
The light has been dark in his tent, And his lamp over him is extinguished.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
The steps of his strength are restricted, And his own counsel casts him down.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
For he is sent into a net by his own feet, And he habitually walks on a snare.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
A trap seizes on the heel, The designing prevails over him.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
His cord is hidden in the earth, And his trap on the path.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Terrors have terrified him all around, And they have scattered him—at his feet.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
His sorrow is hungry, And calamity is ready at his side.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
It consumes the parts of his skin, Death’s firstborn consumes his parts.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
His confidence is drawn from his tent, And it causes him to step to the king of terrors.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
It dwells in his tent—out of his provender, Sulfur is scattered over his habitation.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
From beneath his roots are dried up, And from above his crop is cut off.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
His memorial has perished from the land, And he has no name on the street.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
They thrust him from light to darkness, And cast him out from the habitable earth.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
He has no continuator, Nor successor among his people, And none is remaining in his dwellings.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
At this day, those [in the] west have been astonished, And those [in the] east have taken fright.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Only these [are] dwelling places of the perverse, And this [is] the place God has not known.”

< Ayuba 18 >