< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
آنگاه ایوب پاسخ داد:
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
من از این حرفها زیاد شنیده‌ام. همهٔ شما تسلی‌دهندگان مزاحم هستید.
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
آیا این سخنان بیهودهٔ شما پایانی ندارد؟ چه کسی شما را مجبور کرده این همه بحث کنید؟
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
اگر به جای شما بودم من هم می‌توانستم همین حرفها را بزنم و سرم را تکان داده، شما را به باد انتقاد و ریشخند بگیرم.
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
اما این کار را نمی‌کردم، بلکه طوری صحبت می‌کردم که حرفهایم به شما کمکی بکند. سعی می‌کردم شما را تسلی داده، غمتان را برطرف سازم.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
هر چه سخن می‌گویم ناراحتی و غصه‌ام کاهش نمی‌یابد. اگر هم سکوت کنم و هیچ حرف نزنم، این نیز درد مرا دوا نخواهد کرد.
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
خدایا، تو مرا از زندگی خسته کرده و خانواده‌ام را از من گرفته‌ای.
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
ای خدا، تو آنچنان مرا در سختیها قرار داده‌ای که از من پوست و استخوانی بیش نمانده است و دوستانم این را دلیل گناهان من می‌دانند.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
خدا مرا به چشم یک دشمن نگاه می‌کند و در خشم خود گوشت بدنم را می‌درد.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
مردم مرا مسخره می‌کنند و دور من جمع شده، به صورتم سیلی می‌زنند.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
خدا مرا به دست گناهکاران سپرده است، به دست آنانی که شرور و بدکارند.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
من در کمال آرامش زندگی می‌کردم که ناگاه خدا گلوی مرا گرفت و مرا پاره‌پاره کرد. اکنون نیز مرا هدف تیرهای خود قرار داده است.
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
با بی‌رحمی از هر سو تیرهای خود را به سوی من رها می‌کند و بدن مرا زخمی می‌سازد.
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
او مانند یک جنگجو پی‌درپی به من حمله می‌کند.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
لباس ماتم پوشیده، به خاک ذلت نشسته‌ام.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
از بس گریه کرده‌ام چشمانم سرخ شده و تاریکی بر دیدگانم سایه افکنده است.
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
ولی من بی‌گناهم و دعایم بی‌ریاست.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
ای زمین، خون مرا پنهان نکن؛ بگذار خونم از جانب من بانگ اعتراض برآورد.
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
من شاهدی در آسمان دارم که از من حمایت می‌کند.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
دوستانم مرا مسخره می‌کنند، ولی من اشکهای خود را در حضور خدا می‌ریزم
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
و به او التماس می‌کنم تا مثل شخصی که به حرفهای دوستش گوش می‌دهد، به سخنانم توجه کند.
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
زیرا به‌زودی باید به راهی بروم که از آن بازگشتی نیست.

< Ayuba 16 >