< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Job prit la parole et dit:
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
J’ai souvent entendu pareilles choses; Vous êtes tous des consolateurs fâcheux.
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Quand finiront ces discours en l’air? Pourquoi cette irritation dans tes réponses?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
Moi aussi, je pourrais parler comme vous, Si vous étiez à ma place: Je vous accablerais de paroles, Je secouerais sur vous la tête,
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
Je vous fortifierais de la bouche, Je remuerais les lèvres pour vous soulager.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
Si je parle, mes souffrances ne seront point calmées, Si je me tais, en quoi seront-elles moindres?
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
Maintenant, hélas! Il m’a épuisé… Tu as ravagé toute ma maison;
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
Tu m’as saisi, pour témoigner contre moi; Ma maigreur se lève, et m’accuse en face.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
Il me déchire et me poursuit dans sa fureur, Il grince des dents contre moi, Il m’attaque et me perce de son regard.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
Ils ouvrent la bouche pour me dévorer, Ils m’insultent et me frappent les joues, Ils s’acharnent tous après moi.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
Dieu me livre à la merci des impies, Il me précipite entre les mains des méchants.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
J’étais tranquille, et il m’a secoué, Il m’a saisi par la nuque et m’a brisé, Il a tiré sur moi comme à un but.
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
Ses traits m’environnent de toutes parts; Il me perce les reins sans pitié, Il répand ma bile sur la terre.
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
Il me fait brèche sur brèche, Il fond sur moi comme un guerrier.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
J’ai cousu un sac sur ma peau; J’ai roulé ma tête dans la poussière.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
Les pleurs ont altéré mon visage; L’ombre de la mort est sur mes paupières.
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
Je n’ai pourtant commis aucune violence, Et ma prière fut toujours pure.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
O terre, ne couvre point mon sang, Et que mes cris prennent librement leur essor!
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
Déjà maintenant, mon témoin est dans le ciel, Mon témoin est dans les lieux élevés.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
Mes amis se jouent de moi; C’est Dieu que j’implore avec larmes.
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
Puisse-t-il donner à l’homme raison contre Dieu, Et au fils de l’homme contre ses amis!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
Car le nombre de mes années touche à son terme, Et je m’en irai par un sentier d’où je ne reviendrai pas.

< Ayuba 16 >