< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
“İnsanı kadın doğurur, Günleri sayılı ve sıkıntı doludur.
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
Çiçek gibi açıp solar, Gölge gibi gelip geçer.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
Gözlerini böyle birine mi dikiyorsun, Yargılamak için önüne çağırıyorsun?
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
Kim temizi kirliden çıkarabilir? Hiç kimse!
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Madem insanın günleri belirlenmiş, Aylarının sayısı saptanmış, Sınır koymuşsun, öteye geçemez;
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Gözünü ondan ayır da, Çalışma saatini dolduran gündelikçi gibi rahat etsin.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
“Oysa bir ağaç için umut vardır, Kesilse, yeniden sürgün verir, Eksilmez filizleri.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
Kökü yerde kocasa, Kütüğü toprakta ölse bile,
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
Su kokusu alır almaz filizlenir, Bir fidan gibi dal budak salar.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
İnsan ise ölüp yok olur, Son soluğunu verir ve her şey biter.
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
Suyu akıp giden göl Ya da kuruyan ırmak nasıl çöle dönerse,
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
İnsan da öyle, yatar, bir daha kalkmaz, Gökler yok oluncaya dek uyanmaz, Uyandırılmaz.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
“Keşke beni ölüler diyarına gizlesen, Öfken geçinceye dek saklasan, Bana bir süre versen de, beni sonra anımsasan. (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
İnsan ölür de dirilir mi? Başka biri nöbetimi devralıncaya dek Savaş boyunca umutla beklerdim.
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
Sen çağırırdın, ben yanıtlardım, Ellerinle yaptığın yaratığı özlerdin.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
O zaman adımlarımı sayar, Günahımın hesabını tutmazdın.
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
İsyanımı torbaya koyup mühürler, Suçumu örterdin.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
“Ama dağın yıkılıp çöktüğü, Kayanın yerinden taşındığı,
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
Suyun taşı aşındırdığı, Selin toprağı sürükleyip götürdüğü gibi, İnsanın umudunu yok ediyorsun.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Onu hep yenersin, yok olup gider, Çehresini değiştirir, uzağa gönderirsin.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
Oğulları saygı görür, onun haberi olmaz, Aşağılanırlar, anlamaz.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
Ancak kendi canının acısını duyar, Yalnız kendisi için yas tutar.”

< Ayuba 14 >