< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
Homo, naskita de virino, Havas mallongan vivon kaj abundon da afliktoj.
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
Kiel floro li elkreskas kaj velkas; Li forkuras kiel ombro kaj ne restas.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
Kaj kontraŭ tia Vi malfermas Viajn okulojn, Kaj min Vi vokas al juĝo kun Vi!
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
Ĉu povas purulo deveni de malpurulo? Neniu.
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Se liaj tagoj estas difinitaj, la nombro de liaj monatoj estas ĉe Vi; Vi difinis lian limon, kiun li ne transpasos.
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Deturnu do Vin de li, ke li estu trankvila, Ĝis venos lia tempo, kiun li sopiras kiel dungito.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
Arbo havas esperon, se ĝi estas dehakita, ke ĝi denove ŝanĝiĝos, Kaj ĝi ne ĉesos kreskigi branĉojn.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
Se ĝia radiko maljuniĝis en la tero, Kaj ĝia trunko mortas en polvo,
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
Tamen, eksentinte la odoron de akvo, ĝi denove verdiĝas, Kaj kreskas plue, kvazaŭ ĵus plantita.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
Sed homo mortas kaj malaperas; Kiam la homo finiĝis, kie li estas?
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
Forfluas la akvo el lago, Kaj rivero elĉerpiĝas kaj elsekiĝas:
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
Tiel homo kuŝiĝas, kaj ne plu leviĝas; Tiel longe, kiel la ĉielo ekzistas, ili ne plu vekiĝos, Nek revigliĝos el sia dormado.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
Ho, se Vi kaŝus min en Ŝeol, Se Vi kaŝus min ĝis la momento, kiam pasos Via kolero, Se Vi difinus por mi templimon kaj poste rememorus min! (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
Kiam homo mortas, ĉu li poste povas reviviĝi? Dum la tuta tempo de mia batalado mi atendus, Ĝi venos mia forŝanĝo.
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
Vi vokus, kaj mi respondus al Vi; Vi ekdezirus la faritaĵon de Viaj manoj.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
Nun Vi kalkulas miajn paŝojn; Ne konservu mian pekon;
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
Sigelu en paketo miajn malbonagojn, Kaj kovru mian kulpon.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
Sed monto, kiu falas, malaperas; Kaj roko forŝoviĝas de sia loko;
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
Ŝtonojn forlavas la akvo, Kaj ĝia disverŝiĝo fordronigas la polvon de la tero: Tiel Vi pereigas la esperon de homo.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Vi premas lin ĝis fino, kaj li foriras; Li ŝanĝas sian vizaĝon, kaj Vi forigas lin.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
Se liaj infanoj estas honorataj, li tion ne scias; Se ili estas humiligataj, li tion ne rimarkas.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
Nur lia propra korpo lin doloras, Nur pri sia propra animo li suferas.

< Ayuba 14 >