< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
Man that is born of a woman is of few days, and full of trouble.
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
He cometh forth like a flower, and is cut down: he fleeth also as a shadow, and continueth not.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
And dost thou open thine eyes upon such an one, and bringest me into judgment with thee?
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
Who can bring a clean thing out of an unclean? not one.
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Seeing his days are determined, the number of his months are with thee, thou hast appointed his bounds that he cannot pass;
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Turn from him, that he may rest, till he shall accomplish, as an hireling, his day.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
For there is hope of a tree, if it be cut down, that it will sprout again, and that the tender branch thereof will not cease.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
Though the root thereof wax old in the earth, and the stock thereof die in the ground;
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
Yet through the scent of water it will bud, and bring forth boughs like a plant.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
But man dieth, and wasteth away: yea, man giveth up the ghost, and where is he?
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
As the waters fail from the sea, and the flood decayeth and drieth up:
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
So man lieth down, and riseth not: till the heavens be no more, they shall not awake, nor be raised out of their sleep.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
O that thou wouldest hide me in the grave, that thou wouldest keep me secret, until thy wrath be past, that thou wouldest appoint me a set time, and remember me! (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
If a man die, shall he live again? all the days of my appointed time will I wait, till my change come.
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
Thou shalt call, and I will answer thee: thou wilt have a desire to the work of thine hands.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
For now thou numberest my steps: dost thou not watch over my sin?
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
My transgression is sealed up in a bag, and thou sewest up mine iniquity.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
And surely the mountain falling cometh to nought, and the rock is removed out of his place.
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
The waters wear the stones: thou washest away the things which grow out of the dust of the earth; and thou destroyest the hope of man.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Thou prevailest for ever against him, and he passeth: thou changest his countenance, and sendest him away.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
His sons come to honour, and he knoweth it not; and they are brought low, but he perceiveth it not of them.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
But his flesh upon him shall have pain, and his soul within him shall mourn.

< Ayuba 14 >