< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
Mennesket, født af en Kvinde, hans Liv er stakket, han mættes af Uro;
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
han spirer som Blomsten og visner, flyr som Skyggen, står ikke fast.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
Og på ham vil du rette dit Øje, ham vil du stævne for Retten!
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
Ja, kunde der komme en ren af en uren! Nej, end ikke een!
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Når hans Dages Tal er fastsat, hans Måneder talt hos dig, og du har sat ham en uoverskridelig Grænse,
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
tag så dit Øje fra ham, lad ham i Fred, at han kan nyde sin Dag som en Daglejer!
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
Thi for et Træ er der Håb: Fældes det, skyder det atter, det fattes ej nye Skud;
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
ældes end Roden i Jorden, dør end Stubben i Mulde:
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
lugter det Vand, får det nye Skud, skyder Grene som nyplantet Træ;
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
men dør en Mand, er det ude med ham, udånder Mennesket, hvor er han da?
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
Som Vand løber ud af Søen og Floden svinder og tørres,
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
så lægger Manden sig, rejser sig ikke, vågner ikke, før Himlen forgår, aldrig vækkes han af sin Søvn.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
Tag dog og gem mig i Dødens Rige, skjul mig, indtil din Vrede er ovre, sæt mig en Frist og kom mig i Hu! (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
Om Manden dog døde for atter at leve! Da vented jeg rolig al Stridens Tid, indtil min Afløsning kom;
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
du skulde kalde - og jeg skulde svare længes imod dine Hænders Værk!
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
Derimod tæller du nu mine Skridt, du tilgiver ikke min Synd,
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
forseglet ligger min Brøde i Posen, og over min Skyld har du lukket til.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
Nej, ligesom Bjerget skrider og falder, som Klippen rokkes fra Grunden,
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
som Vandet udhuler Sten og Plaskregn bortskyller Jord, så har du udslukt Menneskets Håb.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
For evigt slår du ham ned, han går bort, skamskænder hans Ansigt og lader ham fare.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
Hans Sønner hædres, han ved det ikke, de synker i Ringhed, han mærker det ikke;
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
ikkun hans eget Kød volder Smerte, ikkun hans egen Sjæl volder Sorg.

< Ayuba 14 >