< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
“Macho yangu yameona hili lote, masikio yangu yamesikia na kulielewa.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Hayo mnayoyajua mimi pia ninayajua; mimi si mtu duni kuliko ninyi.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Lakini ninayo shauku ya kuzungumza na Mwenyezi na kuhojiana shauri langu na Mungu.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Ninyi, hata hivyo, hunipakaza uongo; ninyi ni matabibu wasiofaa kitu, ninyi nyote!
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Laiti wote mngenyamaza kimya! Kwa kuwa kwenu hilo lingekuwa hekima.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Sikieni sasa hoja yangu; sikilizeni kusihi kwangu.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Je, mtazungumza kwa uovu kwa niaba ya Mungu? Je, mtazungumza kwa udanganyifu kwa niaba yake?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Mtamwonyesha upendeleo? Mtamtetea Mungu kwenye mashtaka yake?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Je, ingekuwa vyema Mungu akiwahoji ninyi? Je, mngeweza kumdanganya kama ambavyo mngeweza kuwadanganya wanadamu?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Hakika angewakemea kama mkiwapendelea watu kwa siri.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Je, huo ukuu wake haungewatisha ninyi? Je, hofu yake isingewaangukia ninyi?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Maneno yenu ni mithali za majivu; utetezi wenu ni ngome za udongo wa mfinyanzi.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
“Nyamazeni kimya nipate kusema; kisha na yanipate yatakayonipata.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Kwa nini nijiweke mwenyewe kwenye hatari na kuyaweka maisha yangu mikononi mwangu?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Ingawa ataniua, bado nitamtumaini; hakika nitazitetea njia zangu mbele zake.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Naam, hili litanigeukia kuwa wokovu wangu, kwa maana hakuna mtu asiyemcha Mungu atakayethubutu kuja mbele yake!
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Sikilizeni maneno yangu kwa makini; nayo masikio yenu yaingize kile nisemacho.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Sasa kwamba nimekwisha kutayarisha mambo yangu, ninajua mimi nitahesabiwa kuwa na haki.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Je, kuna yeyote anayeweza kuleta mashtaka dhidi yangu? Kama ndivyo, nitanyamaza kimya na nife.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
“Ee Mungu, unijalie tu mimi haya mambo mawili, nami sitajificha uso wako:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Ondoa mkono wako uwe mbali nami, nawe uache kuniogofya kwa hofu zako kuu.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Niite kwenye shauri nami nitajibu, au niache niseme, nawe upate kujibu.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Ni makosa na dhambi ngapi nilizotenda? Nionyeshe kosa langu na dhambi yangu.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Kwa nini kuuficha uso wako na kunihesabu mimi kuwa adui yako?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Je, utaliadhibu jani lipeperushwalo na upepo? Je, utayasaka makapi makavu?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Kwa kuwa unaandika mambo machungu dhidi yangu na kunifanya nizirithi dhambi za ujana wangu.
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Umeifunga miguu yangu kwenye pingu. Unazichunga kwa makini njia zangu zote kwa kutia alama kwenye nyayo za miguu yangu.
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
“Hivyo mwanadamu huangamia kama kitu kilichooza, kama vazi lililoliwa na nondo.

< Ayuba 13 >