< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Siehe, dies alles hat mein Auge gesehen, mein Ohr gehört und sich gemerkt;
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
was ihr wisset, weiß ich auch; ich stehe nicht hinter euch zurück.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Doch will ich nun zum Allmächtigen reden; mit Gott zu rechten, gelüstet mich.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Ihr streicht ja doch nur Lügenpflaster und seid nichts als Quacksalber.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
O daß ihr doch schweigen könntet, das würde euch als Weisheit angerechnet!
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
So höret nun meine Rechtfertigung und achtet auf die Verteidigung meiner Lippen!
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Wollt ihr Gott zuliebe Unrechtes reden und zu seinen Gunsten lügen?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Wollt ihr seine Person ansehen oder Gottes Sachwalter spielen?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Würde es gut sein, wenn er euch erforschte? Könnt ihr ihn täuschen, wie man Menschen täuscht?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Nein, strafen wird er euch, wenn ihr im Geheimen die Person ansehet!
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Wird nicht seine Majestät euch schrecken und seine Furcht euch überfallen?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Eure Denksprüche sind Aschensprüche, und eure Schutzwehren sind von Lehm.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Schweiget vor mir und laßt mich reden; es gehe über mich, was da wolle!
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Warum sollte ich mein Fleisch in meine Zähne nehmen und mein Leben in meine Hand legen?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Siehe, er soll mich töten; ich habe keine Hoffnung; nur will ich meine Wege ihm ins Angesicht verteidigen.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Auch das schon wird mir zur Rettung dienen; denn kein Gottloser kommt vor ihn.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Höret, höret meine Rede, und meine Erklärung dringe in eure Ohren!
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Gebt acht, ich habe die Verteidigung gerüstet, ich weiß, daß ich Recht bekommen werde.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Wer will noch mit mir rechten? Denn dann wollte ich verstummen und verscheiden.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Nur zweierlei tue nicht an mir, dann will ich mich vor deinem Angesicht nicht verbergen:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Tue deine Hand von mir und erschrecke mich nicht mit deiner Furcht!
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Dann rufe Du, und ich will antworten, oder ich will reden, und Du erwidere mir!
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Wie groß ist meine Sündenschuld? Tue mir meine Übertretungen und Missetaten kund!
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Warum verbirgst du dein Angesicht und hältst mich für deinen Feind?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Verscheuchst du ein verwehtes Blatt und verfolgst einen dürren Halm?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Denn du verschreibst mir Bitteres und lässest mich erben die Sünden meiner Jugend;
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
du legst meine Füße in den Stock und lauerst auf alle meine Schritte und zeichnest dir meine Fußspuren auf,
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
da ich doch wie Moder vergehe, wie ein Kleid, das die Motten fressen!

< Ayuba 13 >