< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
そこでヨブは答えて言った、
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
「まことに、あなたがたのみ、人である、知恵はあなたがたと共に死ぬであろう。
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
しかしわたしも、あなたがたと同様に悟りをもつ。わたしはあなたがたに劣らない。だれがこのような事を知らないだろうか。
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
わたしは神に呼ばわって、聞かれた者であるのに、その友の物笑いとなっている。正しく全き人は物笑いとなる。
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
安らかな者の思いには、不幸な者に対する侮りがあって、足のすべる者を待っている。
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
かすめ奪う者の天幕は栄え、神を怒らす者は安らかである。自分の手に神を携えている者も同様だ。
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
しかし獣に問うてみよ、それはあなたに教える。空の鳥に問うてみよ、それはあなたに告げる。
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
あるいは地の草や木に問うてみよ、彼らはあなたに教える。海の魚もまたあなたに示す。
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
これらすべてのもののうち、いずれか主の手がこれをなしたことを知らぬ者があろうか。
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
すべての生き物の命、およびすべての人の息は彼の手のうちにある。
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
口が食物を味わうように、耳は言葉をわきまえないであろうか。
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
老いた者には知恵があり、命の長い者には悟りがある。
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
知恵と力は神と共にあり、深慮と悟りも彼のものである。
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
彼が破壊すれば、再び建てることができない。彼が人を閉じ込めれば、開き出すことができない。
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
彼が水を止めれば、それはかれ、彼が水を出せば、地をくつがえす。
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
力と深き知恵は彼と共にあり、惑わされる者も惑わす者も彼のものである。
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
彼は議士たちを裸にして連れ行き、さばきびとらを愚かにし、
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
王たちのきずなを解き、彼らの腰に腰帯を巻き、
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
祭司たちを裸にして連れ行き、力ある者を滅ぼし、
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
みずから頼む者たちの言葉を奪い、長老たちの分別を取り去り、
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
君たちの上に侮りを注ぎ、強い者たちの帯を解き、
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
暗やみの中から隠れた事どもをあらわし、暗黒を光に引き出し、
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
国々を大きくし、またこれを滅ぼし、国々を広くし、また捕え行き、
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
地の民の長たちの悟りを奪い、彼らを道なき荒野にさまよわせ、
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
光なき暗やみに手探りさせ、酔うた者のようによろめかせる。

< Ayuba 12 >