< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Job reprit la parole et dit:
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Sans doute, vous êtes l’humanité entière, et avec vous mourra la sagesse!
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Moi aussi, j’ai un cœur comme vous, je ne vous le cède en rien: qui ne, peut user d’arguments pareils?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Je suis la risée des amis, moi qui invoque Dieu et à qui il répond; le juste, l’homme intègre est un objet de dérision!
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
Mépris au malheur! pensent les heureux du monde, voilà ce qui est fait pour ceux dont le pied chancelle!
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Elles jouissent de la paix, les tentes des brigands; parfaite est la sécurité de ceux qui bravent le Tout-Puissant et ne reconnaissent d’autre dieu que leur force.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Toutefois, interroge, de grâce, les bêtes pour qu’elles t’enseignent, les oiseaux du ciel pour qu’ils te mettent au courant.
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Ou bien adresse-toi à la terre pour qu’elle t’instruise, aux poissons de la mer pour qu’ils te donnent leur avis.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Qui ne sait, parmi tous ces êtres, que la main de l’Eternel a tout fait?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
Il tient en sa main le souffle de tout vivant et l’esprit qui anime tout corps humain.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
L’Oreille n’apprécie-t-elle pas les paroles, tout comme le palais déguste les aliments?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
La sagesse est l’apanage des vieillards, les longs jours vont de pair avec la raison.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
C’Est chez lui que se rencontrent la sagesse et la puissance; à lui appartiennent le conseil et l’intelligence.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Voyez, il démolit et personne ne peut rebâtir, il referme la porte sur un homme et personne ne peut l’ouvrir.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Il arrête les eaux, et elles tarissent; il les déchaîne, et elles bouleversent la terre.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
Ses attributs sont la force et la sagesse; il est le maître de celui qui se fourvoie et du séducteur.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Il fait marcher dans la démence les conseillers et livre les juges en proie à la folie.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
II dissout l’autorité des rois et fixe une ceinture autour de leurs reins.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Il frappé d’insanité les prêtres et culbute les puissants.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Il enlève la parole aux orateurs éprouvés et ôte le jugement aux vieillards.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
II déverse la honte sur les nobles, et relâche la ceinture des vaillants.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
Du fond des ténèbres, il fait sortir au jour les choses cachées, et met en pleine lumière ce qui était couvert par l’ombre.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Il grandit les nations, puis il les perd; il les laisse s’étendre, puis il les déporte.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
Il ôte l’intelligence aux chefs des nations et les laisse s’égarer dans des solitudes sans route;
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
là, ils tâtonnent dans une obscurité qui ne laisse percer aucune lueur; et Dieu les fait tituber comme un ivrogne.

< Ayuba 12 >