< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then answered Zophar the Naamathite, and said,
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
Should not the multitude of words be answered? and should a man full of talk be justified?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Should your lies make men hold their peace? and when you mock, shall no man make you ashamed?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
For you have said, My doctrine is pure, and I am clean in your eyes.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
But oh that God would speak, and open his lips against you;
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
And that he would show you the secrets of wisdom, that they are double to that which is! Know therefore that God exacts of you less than your iniquity deserves.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
Can you by searching find out God? can you find out the Almighty to perfection?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
It is as high as heaven; what can you do? deeper than hell; what can you know? (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
The measure thereof is longer than the earth, and broader than the sea.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
If he cut off, and shut up, or gather together, then who can hinder him?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
For he knows vain men: he sees wickedness also; will he not then consider it?
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
For vain men would be wise, though man be born like a wild ass’s colt.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
If you prepare your heart, and stretch out your hands toward him;
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
If iniquity be in your hand, put it far away, and let not wickedness dwell in your tabernacles.
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
For then shall you lift up your face without spot; yes, you shall be steadfast, and shall not fear:
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
Because you shall forget your misery, and remember it as waters that pass away:
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
And your age shall be clearer than the noonday: you shall shine forth, you shall be as the morning.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
And you shall be secure, because there is hope; yes, you shall dig about you, and you shall take your rest in safety.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Also you shall lie down, and none shall make you afraid; yes, many shall make suit to you.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
But the eyes of the wicked shall fail, and they shall not escape, and their hope shall be as the giving up of the ghost.

< Ayuba 11 >