< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then Zophar the Naamathite began speaking and said,
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
“So many words be answered, shouldn't they? Or is a person proved right by doing a lot of talking?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Should all your babbling force people to keep quiet? When you mock, shouldn't someone make you feel ashamed?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
You said, ‘What I teach is the pure truth,’ and ‘in God's eyes I am clean.’
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
If only God would speak up and tell you directly,
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
because then he would explain to you the secrets of wisdom. True wisdom has many sides to it. God's treatment of you is far better than your guilt deserves.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
Can you find out the mysteries of God? Can you discover all the wisdom of the Almighty?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
It is greater than the heavens—what can you do? It is deeper than Sheol—what can you know? (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
It extends farther than the earth, and wider than the sea.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
If God comes and imprisons someone, or assembles the court for judgment, who can stop him?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
For God knows who are deceivers—when he sees someone sin, he pays attention to it.
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
Stupid people will become wise when wild donkeys are born tame!
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
But if you repent and spread out your hands to pray to him,
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
if you get rid of your sins and don't let wickedness continue in your life,
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
then you would be able to hold your head high in innocence, you will be firm and unafraid.
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
You will forget your misery, remembering it only as water under the bridge.
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
Your life will shine brighter than the noonday sun; even darkness will be like the morning.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
You will have confidence because there is hope; you will be protected and rest in safety.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
You will lie down to sleep with no one to frighten you, and many will come asking for your favor.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
But the eyes of the wicked will fail, they will not be able to escape, and their only hope is in death.”

< Ayuba 11 >