< Ayuba 10 >
1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
¡Mi alma está hastiada de mi vida! Daré rienda suelta a mi queja. Hablaré con la amargura de mi alma.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
Diré a ʼElohim: ¡No me condenes! Hazme saber por qué contiendes conmigo.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
¿En verdad, es justo para Ti oprimir, desechar la obra de tus manos y favorecer el designio de los perversos?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
¿Tienes ojos humanos y miras como mira el hombre?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
¿Son tus días como los días del hombre o tus años como los años del hombre,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
para que indagues mi iniquidad e investigues mi pecado?
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Tú sabes que no soy culpable, y que no hay quien libre de tu mano.
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Tus manos me hicieron y me formaron. ¿Y ahora me destruyes?
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Recuerda, te ruego, que del barro me moldeaste. ¿Y al polvo me harás volver?
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
¿No me vertiste como leche y me cuajaste como queso?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
Me cubriste de piel y de carne, con huesos y tendones me tejiste.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Me otorgaste vida y misericordia, y tu cuidado preservó mi espíritu.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Tenías estas cosas ocultas en tu corazón. Yo sé que esto estaba contigo.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
Si peco, Tú me observas, y no me tendrás como limpio de mi culpa.
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
Si soy malo, ¡ay de mí! Y si soy justo, no levantaré mi cabeza. Estoy hastiado de la afrenta y de ver mi aflicción.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
Si mi cabeza se levanta, me cazas como a león y vuelves a mostrar tus proezas en mí.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
Renuevas tus testigos contra mí y aumentas contra mí tu furor como tropas de relevo.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
¿Por qué entonces me sacaste de la matriz? ¡Hubiera yo expirado sin que ningún ojo me viera!
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
Sería como si nunca hubiera existido, llevado del vientre a la tumba.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
¿No son pocos mis días? Cesa pues, y déjame, para que me consuele un poco
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
antes que me vaya a la región tenebrosa de la muerte para no volver,
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
tierra de oscuridad, lóbrega, lugar de sombra de muerte, sin orden, donde la luz es como densa oscuridad.