< Ayuba 10 >
1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
My soul is weary of my life, I will let go my speech against myself, I will speak in the bitterness of my soul.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
I will say to God: Do not condemn me: tell me why thou judgest me so.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Doth it seem good to thee that thou shouldst calumniate me, and oppress me, the work of thy own hands, and help the counsel of the wicked?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Hast thou eyes of flesh: or, shalt thou see as man seeth?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
Are thy days as the days of man, and are thy years as the times of men:
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
That thou shouldst inquire after my iniquity, and search after my sin?
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
And shouldst know that I have done no wicked thing, whereas there is no man that can deliver out of thy hand.
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Thy hands have made me, and fashioned me wholly round about, and dost thou thus cast me down headlong on a sudden?
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Remember, I beseech thee, that thou hast made me as the clay, and thou wilt bring me into dust again.
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Hast thou not milked me as milk, and curdled me like cheese?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
Thou hast clothed me with skin and flesh: thou hast put me together with bones and sinews:
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Thou hast granted me life and mercy, and thy visitation hath preserved my spirit.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Although thou conceal these things in thy heart, yet I know that thou rememberest all things.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
If I have sinned and thou hast spared me for an hour: why dost thou not suffer me to be clean from my iniquity?
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
And if I be wicked, woe unto me: and if just, I shall not lift up my head, being filled with affliction and misery.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
And for pride thou wilt take me as a lioness, and returning thou tormentest me wonderfully.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
Thou renewest thy witnesses against me, and multipliest thy wrath upon me, and pains war against me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Why didst thou bring me forth out of the womb: O that I had been consumed that eye might not see me!
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
I should have been as if I had not been, carried from the womb to the grave.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Shall not the fewness of my days be ended shortly? suffer me, therefore, that I may lament my sorrow a little:
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
Before I go, and return no more, to a land that is dark and covered with the mist of death:
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
A land of misery and darkness, where the shadow of death, and no order, but everlasting horror dwelleth.