< Irmiya 8 >

1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
“At that time,” A declaration of YHWH, “They bring the bones of the kings of Judah, And the bones of its princes, And the bones of the priests, And the bones of the prophets, And the bones of inhabitants of Jerusalem, Out of their graves,
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
And have spread them to sun, and to moon, And to all the host of the heavens, that they have loved, And that they have served, And that they have walked after, And that they have sought, And to which they have bowed themselves, They are not gathered, nor buried, They are for dung on the face of the ground.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
And death is chosen rather than life By all the remnant who are left of this evil family, In all the remaining places, to where I have driven them,” A declaration of YHWH of Hosts.
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
“And you have said to them, Thus said YHWH: Do they fall, and not rise? Does he turn back, and not return?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
Why has this people of Jerusalem Turned back—a continuous backsliding? They have kept hold on deceit, They have refused to turn back.
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
I have given attention, indeed, I listen, They do not speak right, No man has sighed over his wickedness, Saying, What have I done? Everyone has turned to his courses, As a horse is rushing into battle.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
Even a stork in the heavens has known her seasons, And turtle, and swallow, and crane, Have watched the time of their coming, And—My people have not known the judgment of YHWH.
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
How do you say, We [are] wise, And the Law of YHWH [is] with us? Surely, behold, it has worked falsely, The false pen of scribes.
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
The wise have been ashamed, They have been frightened, and are captured, Behold, they kicked against a word of YHWH, And what wisdom do they have?
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
Therefore, I give their wives to others, Their fields to dispossessors, For from the least even to the greatest, Everyone is gaining dishonest gain, From prophet even to priest, everyone is dealing falsely.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
And they heal the breach of the daughter of My people slightly, Saying, Peace, peace! And there is no peace.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
They were ashamed when they did abomination! Indeed, they are not ashamed at all, And they have not known blushing, Therefore, they fall among falling ones, They stumble in the time of their inspection, said YHWH.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
I utterly consume them,” A declaration of YHWH, “There are no grapes in the vine, Indeed, there are no figs in the fig tree, And the leaf has faded, And the strength they have passes from them.
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
Why are we sitting still? Be gathered, and we go into the fortified cities, And we are silent there, For our God YHWH has made us silent, Indeed, He causes us to drink water of gall, For we have sinned against YHWH.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
Looking for peace—and there is no good, For a time of healing, and behold—terror.
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
The snorting of his horses has been heard from Dan, From the voice of the neighings of his mighty ones, All the land has trembled, And they come in and consume the land and its fullness, The city and the inhabitants in it.
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
For behold, I am sending serpents among you, Vipers that have no charmer, And they have bitten you,” A declaration of YHWH.
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
My sorrow [is] beyond comfort, My heart [is] sick in me.
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Behold, the voice of a cry of the daughter of my people from a far-off land, Is YHWH not in Zion? Is her King not in her? “Why have they provoked Me with their carved images, With the vanities of a foreigner?”
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
Harvest has passed, summer has ended, And we have not been saved.
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
For a breach of the daughter of my people I have been broken, I have been dark, Astonishment has seized me.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
Is there no balm in Gilead? Is there no physician there? Why has the health of the daughter of my people not gone up?

< Irmiya 8 >