< Irmiya 6 >

1 “Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
Fuyez, fils de Benjamin, du milieu de Jérusalem! Sonnez la trompette à Tecoa! Arborez des signaux à Beth-Kérém! Car du côté du Nord apparaît la catastrophe, le grand désastre.
2 Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
Bellé, éprise de plaisirs, je la réduis en ruines, la fille de Sion!
3 Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
Vers elle s’avancent des bergers avec leurs troupeaux; ils plantent leurs tentes tout autour d’elle, chacun broutant la place qu’il occupe.
4 “Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
"Engagez l’attaque contre elle! Debout! Donnons l’assaut en plein jour. Hélas! Déjà le jour décline et les ombres du soir s’allongent.
5 Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
Debout! Donnons l’assaut de nuit! Détruisons ses palais!"
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
Oui, ainsi parle l’Eternel-Cebaot: "Taillez des charpentes, élevez des remblais contre Jérusalem; c’est bien cette ville qui doit être châtiée: tout, chez elle, est iniquité.
7 Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
Comme une source laisse jaillir ses eaux, ainsi elle laisse jaillir sa perversité; on n’y entend que violence et oppression, mes yeux n’y voient que souffrances et sévices.
8 Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
Corrige-toi, Jérusalem, sans cela mon âme se détachera de toi; sans cela je ferai de toi une solitude, une terre inhabitée."
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
Ainsi parle l’Eternel-Cebaôt: "Les restes d’Israël seront grappillés jusqu’au bout comme une vigne: passe et repasse ta main comme le vendangeur fouille les sarments."
10 Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
A qui parlerai-je? Qui adjurer, pour qu’on écoute? Voici, leur oreille est bouchée comme par une excroissance, ils ne peuvent prêter d’attention; voici, la parole de l’Eternel est devenue pour eux un objet de mépris, ils n’y prennent aucun goût.
11 Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
Mais moi, je déborde de la colère de l’Eternel, je suis impuissant à la contenir: Répands-la donc sur les enfants dans les rues, sur les groupes de jeunes gens assemblés; car hommes et femmes, anciens et vieillards rassasiés de jours, tous seront capturés.
12 Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
Leurs maisons passeront à d’autres, ainsi que leurs champs et leurs femmes, tout à la fois; car je vais étendre ma main sur les habitants de ce pays, dit l’Eternel.
13 “Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
C’Est que du petit au grand, ils sont tous âpres au gain; depuis le prophète jusqu’au prêtre, tous ils pratiquent le mensonge.
14 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
Ils prétendent guérir le désastre de mon peuple avec des paroles futiles, en disant: "Paix! Paix!" alors qu’il n’y a point de paix.
15 Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
Ils devraient avoir honte des abominations commises par eux; mais ils n’ont plus aucune pudeur, mais ils ne savent plus rougir. Aussi succomberont-ils avec ceux qui succombent à l’heure où j’aurai à les châtier, ils trébucheront, dit l’Eternel.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
Ainsi parle le Seigneur: "Postez-vous sur les routes et regardez, demandez aux sentiers des temps antiques où est le chemin du bonheur. Suivez-le, afin d’y trouver quelque apaisement pour vos âmes! Mais ils ripostent: "Nous ne le suivrons pas."
17 Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
J’Ai établi près de vous des sentinelles: "Attention aux sons de la trompette!" Ils ont répondu: "Nous ne ferons pas attention."
18 Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
Donc écoutez, ô peuples! Apprends, ô assemblée, ce qui les attend!
19 Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
Ecoute, ô terre! Je ferai fondre sur ce peuple une calamité, qui est le fruit de leurs mauvais desseins. car il n’a prêté nulle attention à mes paroles, et mon enseignement, il l’a rejeté.
20 Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
A quoi me sert l’encens venu de Saba, et la canne exquise des pays lointains? Vos holocaustes ne me plaisent pas, vos sacrifices n’ont pas d’agrément pour moi.
21 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
C’Est pourquoi, déclare l’Eternel, je vais dresser contre ce peuple des embûches; ensemble, parents et enfants s’y heurteront, voisins et amis y périront.
22 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
Ainsi parle l’Eternel: Voici, une nation arrive des contrées du Nord, un grand peuple surgit des extrémités de la terre.
23 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
Il est armé d’arcs et de lances; il est cruel et sans pitié; sa voix est mugissante comme la mer, il est monté sur des chevaux, rangé en bataille contre toi comme des braves, ô fille de Sion.
24 Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Sa renommée est arrivée jusqu’à nous, et nos mains sont devenues défaillantes, l’effroi s’est emparé de nous, une angoisse comme celle d’une femme qui enfante.
25 Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
Ne sortez pas dans les champs, ne vous avancez pas sur les routes, car l’ennemi est en armes, la terreur règne aux alentours.
26 Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
Fille de mon peuple! Ceins-toi d’un cilice, roule-toi dans la cendre, organisa un deuil comme pour un fils unique, d’amères complaintes; car soudainement l’envahisseur fondra sur nous.
27 “Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
Tel qu’une tour d’observation, je t’ai établi au milieu de mon peuple, tel qu’une citadelle, afin que tu connaisses et apprécies leurs voies.
28 Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
Tous sont d’incorrigibles rebelles, propagateurs de calomnies, durs comme l’airain et le fer; tous sont malfaisants.
29 Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
Le soufflet da forge a soufflé; par l’action du feu, le plomb devait disparaître; mais vainement on a fondu et refondu, les scories ne se sont pas détachées.
30 Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”
On les a appelés "argent de rebut," car l’Eternel les a mis au rebut.

< Irmiya 6 >