< Irmiya 5 >

1 “Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
Courez çà et là par les rues de Jérusalem, et regardez et sachez et cherchez dans ses places si vous trouvez un homme, s’il y a quelqu’un qui fasse ce qui est droit, qui cherche la fidélité, et je pardonnerai à la ville.
2 Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
Et s’ils disent: L’Éternel est vivant! en cela même, ils jurent faussement.
3 Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
Éternel! tes yeux ne [regardent-ils] pas à la fidélité? Tu les as frappés, mais ils n’en ont point ressenti de douleur; tu les as consumés, ils ont refusé de recevoir la correction; ils ont rendu leurs faces plus dures qu’un roc, ils ont refusé de revenir.
4 Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
Et j’ai dit: Voilà, ce sont de pauvres gens, ce sont des fous; car ils ne connaissent pas la voie de l’Éternel, le jugement de leur Dieu.
5 Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
Je m’en irai vers les grands, et je leur parlerai; car eux, ils connaissent la voie de l’Éternel, le jugement de leur Dieu; mais ceux-ci, tous ensemble, ont brisé le joug, rompu les liens.
6 Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
C’est pourquoi un lion de la forêt les frappera, un loup du soir les ravagera; le léopard veille devant leurs villes, quiconque en sort est déchiré; car leurs transgressions sont multipliées, leurs infidélités se sont renforcées.
7 “Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
Pourquoi te pardonnerai-je? Tes fils m’ont abandonné, et ils jurent par ce qui n’est pas Dieu; je les ai rassasiés, et ils ont commis adultère, et sont allés en troupe dans la maison de la prostituée.
8 An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
Chevaux bien nourris, ils courent çà et là, chacun hennit après la femme de son prochain.
9 Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
Ne punirais-je pas de telles choses? dit l’Éternel; et mon âme ne se vengerait-elle pas d’une nation comme celle-là?
10 “Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
Montez sur ses murailles, et détruisez! mais ne détruisez pas entièrement; ôtez ses créneaux, car ils ne sont pas à l’Éternel;
11 Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
car la maison d’Israël et la maison de Juda ont agi très perfidement envers moi, dit l’Éternel.
12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
Ils ont renié l’Éternel, et ont dit: Il n’est pas! et le mal ne viendra pas sur nous; nous ne verrons ni l’épée ni la famine,
13 Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
et les prophètes seront du vent, et la parole n’est pas en eux: ainsi leur sera-t-il fait.
14 Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
C’est pourquoi, ainsi dit l’Éternel, le Dieu des armées: Parce que vous avez prononcé cette parole, voici, je ferai que mes paroles dans ta bouche seront du feu, et ce peuple sera le bois, et le [feu] les consumera.
15 Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
Voici, je fais venir de loin une nation contre vous, maison d’Israël, dit l’Éternel, une nation puissante, une nation ancienne, une nation dont tu ne sais pas la langue, et dont tu ne comprends pas la parole.
16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
Son carquois est comme un sépulcre ouvert, ils sont tous des hommes vaillants.
17 Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
Elle dévorera ta moisson et ton pain, elle dévorera tes fils et tes filles, elle dévorera ton menu et ton gros bétail, elle dévorera ta vigne et ton figuier, elle détruira par l’épée tes villes fortes sur lesquelles tu te confiais.
18 “Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
Mais, même en ces jours-là, dit l’Éternel, je ne vous détruirai pas entièrement.
19 Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
Et il arrivera que, quand vous direz: Pourquoi l’Éternel, notre Dieu, nous a-t-il fait toutes ces choses? tu leur diras: Comme vous m’avez abandonné et que vous avez servi des dieux étrangers dans votre pays, ainsi vous servirez les étrangers dans un pays qui n’est pas le vôtre.
20 “Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
Annoncez ceci dans la maison de Jacob, et faites-le entendre dans Juda, disant:
21 Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
Écoutez pourtant ceci, peuple insensé et sans intelligence, qui avez des yeux et ne voyez pas, qui avez des oreilles et n’entendez pas.
22 Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
Ne me craindrez-vous pas, dit l’Éternel, ne tremblerez-vous pas devant moi, qui ai mis le sable pour limite à la mer, statut perpétuel, qu’elle n’outrepassera pas? Ses vagues se soulèvent, mais elles ne prévaudront pas; et elles bruient, mais elles ne l’outrepasseront pas.
23 Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
Mais ce peuple-ci a un cœur indocile et rebelle; ils se sont détournés, et s’en sont allés;
24 Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
et ils n’ont pas dit dans leur cœur: Craignons pourtant l’Éternel, notre Dieu, qui donne les pluies en leur temps, la pluie de la première saison et la pluie de la dernière saison, [et] qui nous garde les semaines ordonnées de la moisson.
25 Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
Vos iniquités ont détourné ces choses, et vos péchés ont retenu de vous le bien.
26 “A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
Car il se trouve des méchants parmi mon peuple; ils épient comme l’oiseleur qui se baisse, ils posent des pièges, ils prennent des hommes.
27 Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
Comme une cage est pleine d’oiseaux, ainsi leurs maisons sont pleines de fraude; c’est pourquoi ils sont devenus grands et se sont enrichis.
28 suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
Ils sont devenus gras et luisants, aussi ils débordent de méchancetés; ils ne jugent pas la cause, la cause de l’orphelin, et ils prospèrent; et ils ne font pas droit aux pauvres.
29 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
Ne punirais-je pas de telles choses? dit l’Éternel; mon âme ne se vengerait-elle pas d’une nation comme celle-là?
30 “Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
Une chose étonnante et horrible est arrivée dans le pays:
31 Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?
les prophètes prophétisent avec mensonge, et les sacrificateurs dominent par leur moyen; et mon peuple l’aime ainsi. Et que ferez-vous à la fin?

< Irmiya 5 >