< Irmiya 47 >

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
کلام خداوند درباره فلسطینیان که برارمیا نبی نازل شد قبل از آنکه فرعون غزه را مغلوب بسازد.۱
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
خداوند چنین می‌گوید: «اینک آبها از شمال برمی آید و مثل نهری سیلان می‌کند و زمین را با آنچه در آن است و شهر وساکنانش را درمی گیرد. و مردمان فریادبرمی آورند و جمیع سکنه زمین ولوله می‌نمایند۲
3 da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
از صدای سمهای اسبان زورآورش و ازغوغای ارابه هایش و شورش چرخهایش. وپدران به‌سبب سستی دستهای خود به فرزندان خویش اعتنا نمی کنند.۳
4 Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
به‌سبب روزی که برای هلاکت جمیع فلسطینیان می‌آید که هرنصرت کننده‌ای را که باقی می‌ماند از صور وصیدون منقطع خواهد ساخت. زیرا خداوندفلسطینیان یعنی بقیه جزیره کفتور را هلاک خواهد ساخت.۴
5 Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
اهل غزه بریده مو گشته‌اند واشقلون و بقیه وادی ایشان هلاک شده است. تا به کی بدن خود را خواهی خراشید؟۵
6 “Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
آه‌ای شمشیر خداوند تا به کی آرام نخواهی گرفت؟ به غلاف خود برگشته، مستریح و آرام شو.۶
7 Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”
چگونه می‌توانی آرام بگیری، با آنکه خداوند تو را بر اشقلون و بر ساحل دریا مامور فرموده و تو را به آنجا تعیین نموده است؟»۷

< Irmiya 47 >