< Irmiya 47 >
1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
Das Wort Jehovahs, das an den Propheten Jirmejahu geschah wider die Philister, ehe denn Pharao Gazah schlug.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
So spricht Jehovah: Siehe, Wasser steigen auf von Mitternacht und werden zu einem überflutenden Bache, und sie überfluten das Land und seine Fülle, die Stadt und die darin wohnen; und schreien werden die Menschen und heulen wird alles, was im Lande wohnt.
3 da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
Ob dem Lärm des Stampfens der Hufe ihrer Gewaltigen, ob dem Gerassel ihrer Streitwagen und dem Getümmel ihrer Räder wenden sich Väter nicht zu den Söhnen vor Erschlaffung ihrer Hände.
4 Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
Ob dem Tag, der da kommen wird, alle Philister zu verheeren, auszurotten Zor und Zidon, und allen Rest, der beisteht, denn Jehovah verheert die Philister, den Überrest der Insel Kaphthor.
5 Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
Kahlheit kommt über Gazah, Aschkalon geht unter, der Überrest ihres Talgrundes. Bis wann wirst du dich ritzen?
6 “Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
O Schwert Jehovahs, bis wann wirst du nicht rasten? Ziehe dich zurück in deine Scheide. Ruhe dich aus und sei stille.
7 Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”
Wie kannst du rasten? Und Jehovah hat ihm wider Aschkalon geboten und an des Meeres Gestade es beschieden.