< Irmiya 47 >
1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
Telle est la communication que fit l’Eternel au prophète Jérémie concernant les Philistins, avant la défaite infligée par Pharaon à Gaza:
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
"Ainsi parle l’Eternel: Voici que des flots s’avancent du Nord et deviennent un torrent impétueux, submergeant la terre et ce qu’elle renferme, les villes et ceux qui y demeurent. Les hommes poussent des cris et tous les habitants du pays se lamentent.
3 da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
Au trot bruyant des sabots des fiers coursiers, au roulement des chars, au fracas de leurs roues, les pères n’ont plus de regard pour leurs enfants, tant ils sont abattus,
4 Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
à cause de l’arrivée de ce jour qui verra ruiner tous les Philistins, enlever à Tyr et à Sidon leurs derniers auxiliaires, car l’Eternel veut perdre les Philistins, ces émigrés de l’île de Caphtor.
5 Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
Gaza est atteinte de calvitie, Ascalon est anéantie avec le reste de leur plaine jusqu’à quand te feras-tu des incisions?
6 “Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
Holà! Glaive du Seigneur, quand donc te reposeras-tu enfin? Rentre dans ton fourreau, apaise-toi, fais trève!
7 Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”
Mais comment se tiendrait-il coi, alors que l’Eternel lui a donné des ordres? A Ascalon et sur les bords de la mer, il lui a assigné un rendez-vous."