< Irmiya 43 >

1 Sa’ad da Irmiya ya gama faɗa wa mutane dukan maganar Ubangiji Allahnsu, duk abin da Ubangiji ya aike shi ya faɗa musu,
E succedeu que, acabando Jeremias de fallar a todo o povo todas as palavras do Senhor Deus d'elles, com as quaes o Senhor Deus d'elles lh'o havia enviado, para que lhes dissesse todas estas palavras,
2 Azariya ɗan Hoshahiya da Yohanan ɗan Kareya da dukan masu ɗaga kai suka ce wa Irmiya, “Kana ƙarya ne! Ubangiji Allahnmu bai aike ka ka ce, ‘Kada ku tafi Masar don ku zauna a can.’
Então disse Azarias, filho de Hosaias, e Johanan, filho de Careah, e todos os homens soberbos, dizendo a Jeremias: Tu dizes mentiras; o Senhor nosso Deus não te enviou a dizer: Não entreis no Egypto, para lá peregrinar:
3 Amma Baruk ɗan Neriya yana zuga ka a kanmu don ka ba da mu ga Babiloniyawa, don su kashe mu ko su kai mu zaman bauta a Babilon.”
Antes Baruch, filho de Nerias, te incita contra nós, para entregar-nos na mão dos chaldeos, para nos matarem, ou para nos transportarem para Babylonia.
4 Saboda haka Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da dukan mutane suka yi rashin biyayya ga umarnin Ubangiji da su zauna a ƙasar Yahuda.
Não obedeceu pois Johanan, filho de Careah, nem nenhum de todos os principes dos exercitos, nem todo o povo, á voz do Senhor, para ficarem na terra de Judah.
5 A maimako, Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe raguwar Yahuda waɗanda suka dawo su zauna a ƙasar Yahuda daga dukan al’umman inda aka kora su.
Antes tomou Johanan, filho de Careah, e todos os principes dos exercitos a todo o resto de Judah, que havia voltado d'entre todas as nações, para onde haviam sido lançados, para peregrinarem na terra de Judah;
6 Suka kuma kwashe dukan maza, mata da yara da’ya’yan sarki mata waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari tare da Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da Irmiya annabi da kuma Baruk ɗan Neriya.
Os homens, e as mulheres, e os meninos, e as filhas do rei, e a toda a alma que deixara Nebuzaradan, capitão dos da guarda, com Gedalias, filho de Ahicam, filho de Saphan; como tambem a Jeremias, o propheta, e a Baruch, filho de Nerias:
7 Saboda haka suka shiga Masar cikin rashin biyayya ga Ubangiji suka tafi har can Tafanes.
E entraram na terra do Egypto, porque não obedeceram á voz do Senhor; e vieram até Tahpanhes.
8 A Tafanes maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Então veiu a palavra do Senhor a Jeremias, em Tahpanhes, dizendo:
9 “Yayinda Yahudawa suna kallo, ka ɗauki waɗansu manyan duwatsu tare da kai ka kuma binne su cikin yumɓu a tubalin dakalin ƙofar shiga fadar Fir’auna a Tafanes.
Toma na tua mão pedras grandes, e esconde-as entre o barro no forno que está á porta da casa de Pharaó em Tahpanhes, perante os olhos de homens judeos.
10 Sa’an nan ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, zan aika wa bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon, zan kuma sa kursiyinsa a kan waɗannan duwatsun da na binne a nan; zai fadada bukkar mulkinsa a bisansu.
E dize-lhes: Assim diz o Senhor dos exercitos, Deus de Israel: Eis que eu enviarei, e tomarei a Nabucodonozor, rei de Babylonia, meu servo, e porei o seu throno sobre estas pedras que escondi; e estenderá a sua tenda real sobre ellas.
11 Zai zo ya yaƙi Masar, ya kawo mutuwa ga waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa, zaman bauta ga waɗanda aka ƙaddara musu zaman bauta, da kuma takobi ga waɗanda aka ƙaddara su mutu ta takobi.
E virá, e ferirá a terra do Egypto: quem para a morte, para a morte; e quem para o captiveiro, para o captiveiro; e quem para a espada, para a espada.
12 Zai sa wuta wa haikalan allolin Masar; zai ƙone haikalansu yă kuma kwashe allolinsu bayi. Kamar yadda makiyayi yakan yafa mayafinsa kewaye da shi, haka zai yafa Masar kewaye da kansa ya kuma tashi a wurin babu abin da ya same shi.
E porei fogo ás casas dos deuses do Egypto, e queimal-os-ha, e leval-os-ha captivos; e vestir-se-ha da terra do Egypto, como se veste o pastor do seu vestido, e sairá d'ali em paz.
13 A can cikin haikalin rana a Masar zai rushe al’amudan duwatsu yă kuma ƙone haikalan allolin Masar.’”
E quebrará as estatuas de Beth-semes, que está na terra do Egypto; e as casas dos deuses do Egypto queimará a fogo.

< Irmiya 43 >