< Irmiya 42 >

1 Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
Tous les chefs des troupes, Jochanan, fils de Karéach, Jezania, fils d’Hosée, et tout le peuple, depuis le plus petit jusqu’au plus grand, s’avancèrent,
2 Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
et dirent à Jérémie, le prophète: Que nos supplications soient favorablement reçues devant toi! Intercède en notre faveur auprès de l’Éternel, ton Dieu, en faveur de tous ceux qui restent, car nous étions beaucoup, et nous restons en petit nombre, comme tes yeux le voient;
3 Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
et que l’Éternel, ton Dieu, nous montre le chemin que nous devons suivre, et ce que nous avons à faire!
4 Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
Jérémie, le prophète, leur dit: J’entends; voici je vais prier l’Éternel, votre Dieu, selon votre demande; et je vous ferai connaître, sans rien vous cacher, tout ce que l’Éternel vous répondra.
5 Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
Et ils dirent à Jérémie: Que l’Éternel soit contre nous un témoin véritable et fidèle, si nous ne faisons pas tout ce que l’Éternel, ton Dieu, te chargera de nous dire!
6 Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
Que ce soit du bien ou du mal, nous obéirons à la voix de l’Éternel, notre Dieu, vers qui nous t’envoyons, afin que nous soyons heureux, si nous obéissons à la voix de l’Éternel, notre Dieu.
7 Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
Dix jours après, la parole de l’Éternel fut adressée à Jérémie.
8 Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
Et Jérémie appela Jochanan, fils de Karéach, tous les chefs des troupes qui étaient avec lui, et tout le peuple, depuis le plus petit jusqu’au plus grand.
9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
Il leur dit: Ainsi parle l’Éternel, le Dieu d’Israël, vers qui vous m’avez envoyé, pour que je lui présente vos supplications:
10 ‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
Si vous restez dans ce pays, je vous y établirai et je ne vous détruirai pas, je vous planterai et je ne vous arracherai pas; car je me repens du mal que je vous ai fait.
11 Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
Ne craignez pas le roi de Babylone, dont vous avez peur; ne le craignez pas, dit l’Éternel, car je suis avec vous pour vous sauver et vous délivrer de sa main;
12 Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
je lui inspirerai de la compassion pour vous, et il aura pitié de vous, et il vous laissera demeurer dans votre pays.
13 “Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
Mais si vous n’obéissez pas à la voix de l’Éternel, votre Dieu,
14 in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
et si vous dites: Nous ne resterons pas dans ce pays, non, nous irons au pays d’Égypte, où nous ne verrons point de guerre, où nous n’entendrons pas le son de la trompette, où nous ne manquerons pas de pain, et c’est là que nous habiterons,
15 to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
alors écoutez la parole de l’Éternel, restes de Juda! Ainsi parle l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: Si vous tournez le visage pour aller en Égypte, si vous y allez demeurer,
16 takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
l’épée que vous redoutez vous atteindra là au pays d’Égypte, la famine que vous craignez s’attachera à vous là en Égypte, et vous y mourrez.
17 Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
Tous ceux qui tourneront le visage pour aller en Égypte, afin d’y demeurer, mourront par l’épée, par la famine ou par la peste, et nul n’échappera, ne fuira, devant les malheurs que je ferai venir sur eux.
18 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
Car ainsi parle l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: De même que ma colère et ma fureur se sont répandues sur les habitants de Jérusalem, de même ma fureur se répandra sur vous, si vous allez en Égypte; vous serez un sujet d’exécration, d’épouvante, de malédiction et d’opprobre, et vous ne verrez plus ce lieu.
19 “Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
Restes de Juda, l’Éternel vous dit: N’allez pas en Égypte! Sachez que je vous le défends aujourd’hui.
20 cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
Vous vous trompez vous-mêmes, car vous m’avez envoyé vers l’Éternel, votre Dieu, en disant: Intercède en notre faveur auprès de l’Éternel, notre Dieu, fais-nous connaître tout ce que l’Éternel, notre Dieu, dira, et nous le ferons.
21 Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
Je vous l’ai déclaré aujourd’hui; mais vous n’écoutez pas la voix de l’Éternel, votre Dieu, ni tout ce qu’il m’a chargé de vous dire.
22 Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”
Sachez maintenant que vous mourrez par l’épée, par la famine ou par la peste, dans le lieu où vous voulez aller pour y demeurer.

< Irmiya 42 >