< Irmiya 38 >

1 Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
Alors Saphatias, fils de Mathan, Gédélias, fils de Phassur, Juchal, fils de Sélémias, et Phassur, fils de Melchias, entendirent les paroles que Jérémie adressait à tout le peuple, en disant:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
« Ainsi parle Yahweh: Celui qui restera dans cette ville mourra par l’épée, par la famine ou par la peste; mais celui qui sortira pour se rendre aux Chaldéens vivra; il aura la vie pour butin, et il vivra.
3 Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
Ainsi parle Yahweh: Cette ville sera livrée à l’armée du roi de Babylone, et il la prendra. »
4 Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
Et les chefs dirent au roi: « Qu’on fasse donc mourir cet homme! Car il décourage les hommes de guerre qui restent dans la ville, et tout le peuple, en leur tenant ces discours. Car cet homme ne cherche pas le bien de ce peuple, mais son malheur. »
5 “Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
Et le roi Sédécias dit: « Il est en votre pouvoir, car le roi ne peut rien contre vous. »
6 Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
Alors ils prirent Jérémie et le descendirent dans la citerne de Melchias, fils du roi, dans la cour de garde; ils descendirent Jérémie avec des cordes dans la citerne; il n’y avait pas d’eau, mais de la boue. Et Jérémie enfonça dans la boue.
7 Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
Abdémélech, l’Ethiopien, eunuque de la maison du roi, apprit qu’on avait mis Jérémie dans la citerne. — Or le roi était assis à la porte de Benjamin. —
8 Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
Abdémélech sortit de la maison du roi, et il parla au roi en ces termes:
9 “Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
« O roi, mon seigneur, ces hommes ont mal agi en traitant ainsi Jérémie, le prophète; ils l’ont descendu dans la citerne; il mourra de faim sur place, car il n’y a plus de pain dans la ville.”
10 Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
Et le roi donna cet ordre à Abdémélech, l’Ethiopien: « Prends ici trente hommes avec toi, et fais remonter de la citerne Jérémie le prophète, avant qu’il ne meure. »
11 Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
Abdémélech prit donc avec lui ces hommes et entra dans la maison du roi, au-dessous de la trésorerie. Il y prit des linges usés et de vieilles hardes, et il les fit passer avec des cordes à Jérémie dans la citerne.
12 Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
Et Abdémélech, l’Ethiopien, dit à Jérémie: « Mets ces linges usés et ces hardes sous tes aisselles, par-dessous les cordes. » Jérémie fit ainsi.
13 suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
Et ils le tirèrent avec des cordes, et le firent remonter de la citerne. Et Jérémie demeura dans la cour de garde.
14 Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
Alors le roi Sédécias envoya prendre Jérémie, le prophète, et le fit venir vers lui à la troisième entrée de la maison de Yahweh. Et le roi dit à Jérémie: « J’ai une chose à te demander; ne me cache rien! »
15 Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
Et Jérémie dit à Sédécias: « Si je te la dis, ne me feras-tu pas sûrement mourir? Et si je te donne un conseil, tu ne m’écouteras pas. »
16 Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
Le roi Sédécias fit en secret ce serment à Jérémie: « Yahweh est vivant, lui qui nous a donné cette vie! Je ne te ferai pas mourir, et je ne te livrerai pas aux mains de ces hommes qui en veulent à ta vie. »
17 Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
Alors Jérémie dit à Sédécias: « Ainsi parle Yahweh des armées, Dieu d’Israël: Si tu sors pour te rendre aux chefs du roi de Babylone, tu auras la vie sauve, et cette ville ne sera pas brûlée; tu vivras, toi et ta maison.
18 Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
Mais si tu ne sors pas vers les chefs du roi de Babylone, cette ville sera livrée aux mains des Chaldéens, qui la brûleront; et toi tu ne leur échapperas point. »
19 Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
Et le roi Sédécias dit à Jérémie: « Je crains les Judéens qui ont passé aux Chaldéens; on me livrera à eux, et ils se joueront de moi. »
20 Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
Jérémie répondit: « On ne te livrera pas. Ecoute donc la voix de Yahweh dans ce que je te dis; tu t’en trouveras bien, et tu auras la vie sauve.
21 Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
Mais si tu refuses de sortir, voici ce que Yahweh m’a révélé:
22 Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
Voici que toutes les femmes qui sont restées de la maison du roi de Juda, seront menées aux chefs du roi de Babylone, et elles te diront: Tes amis t’ont séduit et dominé; tes pieds se sont enfoncés dans la boue, et eux se sont esquivés.
23 “Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
Et on mènera toutes tes femmes et tes enfants aux Chaldéens, et toi-même tu ne leur échapperas pas; mais tu seras pris par le roi de Babylone, et tu auras brûlé cette ville. »
24 Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
Et Sédécias dit à Jérémie: « Que personne ne sache rien de cet entretien, et tu ne mourras point.
25 In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
Si les chefs apprennent que j’ai parlé avec toi, et qu’ils viennent te dire: Déclare-nous ce que tu as dit au roi et ce que le roi t’a dit; ne nous cache rien, et nous ne te ferons pas mourir,
26 sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
tu leur répondras: J’ai présenté ma supplication au roi pour qu’il ne me fasse pas retourner dans la maison de Jonathan, où je mourrais. »
27 Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
Tous les chefs vinrent en effet vers Jérémie et le questionnèrent; il leur répondit entièrement selon ces paroles que le roi lui avait prescrites; et ils le laissèrent en repos, car l’entretien n’avait pas été entendu.
28 Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,
Ainsi Jérémie resta dans la cour de garde jusqu’à la prise de Jérusalem, et il y était lorsque Jérusalem fut prise.

< Irmiya 38 >