< Irmiya 34 >

1 Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
The word that came to Jeremiah from the Lord, when Nebuchadnezzar, the king of Babylon, and his entire army, and all the kingdoms of the earth that were under the authority of his hand, and all the people were making war against Jerusalem and against all of its cities, saying:
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
“Thus says the Lord, the God of Israel: Go, and speak to Zedekiah, the king of Judah. And you shall say to him: Thus says the Lord: Behold, I will deliver this city into the hands of the king of Babylon, and he will burn it with fire.
3 Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
And you will not escape from his hand. Instead, you will be overtaken and captured, and you will be delivered into his hand. And your eyes will see the eyes of the king of Babylon, and his mouth will speak with your mouth, and you will enter into Babylon.
4 “‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
Even so, listen to the word of the Lord, Zedekiah, king of Judah: Thus says the Lord to you: You will not die by the sword.
5 za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
Instead, you will die in peace. And, in accord with the burnings of your fathers, the former kings who were before you, so will they burn you. And they will mourn you, saying: ‘Alas, lord!’ For I have spoken the word, says the Lord.”
6 Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
And Jeremiah, the prophet, spoke all these words to Zedekiah, the king of Judah, in Jerusalem.
7 yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
And the army of the king of Babylon fought against Jerusalem and against all the cities of Judah that remained, against Lachish and against Azekah. For only these remained out of the cities of Judah that were fortified cities.
8 Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
The word that came to Jeremiah from the Lord, after king Zedekiah had struck a pact with all the people in Jerusalem, proclaiming
9 Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
that each one should release his man servant, and each one his woman servant, as a free Hebrew man and a free Hebrew woman, and that they should never be rulers over them, that is, over the Jews, their own brothers.
10 Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
Then all the leaders and all the people who entered into the pact, heard that each one should release his man servant, and each one his woman servant, to be free, and that they should no longer rule over them. Therefore, they listened, and they released them.
11 Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
But later on, they turned back. And they took back again their man servants and their woman servants, whom they had released to be free. And they subjugated them as male and female servants.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
And the word of the Lord came to Jeremiah from the Lord, saying:
13 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
“Thus says the Lord, the God of Israel: I struck a pact with your fathers in the day when I led them away from the land of Egypt, from the house of servitude, saying:
14 ‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
‘When seven years have been completed, let each one release his brother, a Hebrew, who had been sold to him. And so he will serve you for six years, and then you shall release him to be free from you.’ But your fathers did not listen to me, nor did they incline their ear.
15 Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
And today you converted, and you did what is right in my eyes, so that you proclaimed liberty, each one to his friend. And you entered into a pact in my sight, in the house in which and over which my name is invoked.
16 Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
But now you have turned back, and you have stained my name. For you have led back again, each one his man servant, and each one his woman servant, whom you had released so that they would be free and under their own authority. And you have subjugated them, so that they would be your servants and handmaids.”
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
Because of this, thus says the Lord: “You have not heeded me, though you proclaimed liberty, each one to his brother and each one to his friend. Behold, I am proclaiming a liberty for you, says the Lord, to the sword, to pestilence, and to famine. And I will cause you to be removed to all the kingdoms of the earth.
18 Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
And I will give over the men who have betrayed my covenant, and who have not observed the words of the covenant, to which they assented in my sight when they cut the calf into two parts and passed between its parts:
19 Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
the leaders of Judah, and the leaders of Jerusalem, the eunuchs and the priests, and all the people of the land, who have passed between the parts of the calf.
20 zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
And I will give them into the hands of their enemies and into the hands of those who are seeking their life. And their dead bodies will be food for the birds of the air and for the beasts of the earth.
21 “Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
And Zedekiah, the king of Judah, and his leaders, I will give over to the hands of their enemies, and to the hands of those who are seeking their lives, and to the hands of the armies of the king of Babylon, which had withdrawn from you.
22 Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”
Behold, I will command, says the Lord, and I will lead them back to this city, and they will fight against it, and seize it, and set it on fire. And I will make the cities of Judah into a desolation, for there shall be no inhabitant.”

< Irmiya 34 >