< Irmiya 31 >

1 “A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
En ce temps-là, — oracle de Yahweh, — je serai le Dieu de toutes les familles d’Israël, et elles seront mon peuple.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
Ainsi parle Yahweh: Il a trouvé grâce dans le désert, le peuple échappé au glaive; je veux mettre Israël en repos.
3 Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
Yahweh m’est apparu de loin. Je t’ai aimée d’un amour éternel, aussi j’ai prolongé pour toi la miséricorde.
4 Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
Je te bâtirai encore, et tu seras rebâtie, vierge d’Israël; tu te pareras encore en main tes tambourins, et tu t’avanceras au milieu des danses joyeuses.
5 Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
Tu planteras encore tes vignes sur les montagnes de Samarie; ceux qui plantent planteront, et ils recueilleront.
6 Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
Car le jour vient où les gardes crieront sur la montagne d’Ephraïm: « Levez-vous et montons à Sion vers Yahweh notre Dieu. »
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
Car ainsi parle Yahweh: Poussez des cris de joie sur Jacob, éclatez d’allégresse pour la première des nations; faites-vous, entendre, chantez des louanges et dites: « Yahweh, sauve ton peuple, le reste d’Israël! »
8 Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
Voici que je les ramène du pays du septentrion, que je les rassemble des extrémités de la terre. Parmi eux seront l’aveugle et le boiteux, la femme enceinte et celle qui enfante; ils reviendront ici en grande foule.
9 Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
Ils reviendront en pleurant; je les ramènerai au milieu de leurs supplications; je les conduirai aux eaux courantes, par un chemin uni où ils ne broncheront pas; car j’ai été un père à Israël, et Ephraïm est mon premier-né.
10 “Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
Nations, écoutez la parole de Yahweh et annoncez-la aux îles lointaines; dites: « Celui qui a dispersé Israël le rassemblera, et le gardera comme un berger son troupeau.
11 Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
Car Yahweh a racheté Jacob, Il l’a délivré des mains d’un plus fort que lui. »
12 Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
Ils viendront avec des cris de joie sur la hauteur de Sion; ils afflueront vers les biens de Yahweh, vers le blé, vers le vin nouveau, vers l’huile, vers les brebis et les bœufs; leur âme sera comme un jardin arrosé, et ils ne continueront plus de languir.
13 ’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
Alors la jeune fille s’égaiera à la danse, et les jeunes hommes et les vieillards ensemble; je changerai leur deuil en joie, je les consolerai, je les réjouirai après leurs douleurs.
14 Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
Je rassasierai de graisse l’âme des prêtres, et mon peuple se rassasiera de mes biens, — oracle de Yahweh.
15 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
Ainsi parle Yahweh: Une voix a été entendue à Rama, des lamentations et des pleurs amers: Rachel pleurant ses enfants; elle refuse d’être consolée, sur ses enfants, parce qu’ils ne sont plus.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
Ainsi parle Yahweh: Retiens ta voix de gémir, et tes yeux de pleurer. Car ton œuvre aura sa récompense, — oracle de Yahweh: ils reviendront du pays de l’ennemi.
17 Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
Il y a de l’espérance pour tes derniers jours, — oracle de Yahweh, et tes enfants retourneront dans leurs frontières.
18 “Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
J’ai entendu Ephraïm qui gémit: « Tu m’as châtié, et j’ai été châtié, comme un jeune taureau indompté; fais-moi revenir et je reviendrai, car tu es Yahweh mon Dieu!
19 Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
Car après m’être détourné, je me suis repenti, et après avoir compris, j’ai frappé ma cuisse; je suis honteux et confus, car je porte l’opprobre de ma jeunesse. »
20 Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
Ephraïm est-il donc pour moi un fils si cher, un enfant favori? Car chaque fois que je parle contre lui, je me ressouviens encore de lui. Aussi pour lui mes entrailles se sont émues; oui, j’aurai pitié de lui, — oracle de Yahweh.
21 “Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
Dresse pour toi des signaux, pose pour toi des jalons; fais attention à la route, au chemin par lequel tu as marché. Reviens, vierge d’Israël, reviens ici, dans tes villes.
22 Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
Jusques à quand seras-tu errante, fille rebelle? Car Yahweh a créé une chose nouvelle sur la terre: une femme entourera un homme.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
Ainsi parle Yahweh des armées, Dieu d’Israël: On dira encore cette parole sur la terre de Juda et dans ses villes, quand je ramènerai leurs captifs: « Que Yahweh te bénisse, demeure de la justice, montagne de la sainteté! »
24 Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
Là habiteront Juda et toutes ses villes, les laboureurs et ceux qui conduisent les troupeaux.
25 Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
Car j’abreuverai l’âme altérée, et je rassasierai l’âme languissante.
26 A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
Sur cela je me suis réveillé, et j’ai vu que mon sommeil avait été doux.
27 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
Des jours viennent — oracle de Yahweh, où j’ensemencerai la maison d’Israël et la maison de Juda d’une semence d’homme et d’une semence d’animaux.
28 Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
Et il arrivera: comme j’ai veillé sur eux pour arracher et pour abattre, pour ruiner, pour détruire et pour faire du mal, ainsi je veillerai sur eux pour bâtir et pour planter, — oracle de Yahweh.
29 “A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
En ces jours-là on ne dira plus: « Les pères ont mangé des raisins verts, et les dents des fils en sont agacées. »
30 A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
Mais chacun mourra pour son iniquité; tout homme qui mangera des raisins verts, ses dents en seront agacées.
31 “Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Voici que des jours viennent, — oracle de Yahweh, où je concluerai avec la maison d’Israël et avec la maison de Juda une alliance nouvelle,
32 Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
non comme l’alliance que je conclus avec leurs pères, le jour où je les pris par la main pour les faire sortir du pays d’Égypte, alliance qu’eux ont rompue, quoique je fusse leur époux.
33 “Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
Car voici l’alliance que je ferai avec la maison d’Israël, après ces jours-là, — oracle de Yahweh: Je mettrai ma loi au dedans d’eux, et je l’écrirai sur leur cœur; et je serai leur Dieu, et ils seront mon peuple.
34 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
Un homme n’enseignera plus son prochain, ni un homme son frère, en disant: « Connaissez Yahweh! » Car ils me connaîtront tous, depuis les petits jusqu’aux grands, — oracle de Yahweh. Car je pardonnerai leur iniquité, et je ne me souviendrai plus de leur péché.
35 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Ainsi parle Yahweh, qui donne le soleil pour éclairer pendant le jour, et trace des lois à la lune et aux étoiles pour éclairer pendant la nuit, qui soulève la mer et ses flots mugissent, — Yahweh des armées est son nom: —
36 “In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
Si jamais ces lois cessent devant moi, — oracle de Yahweh, alors aussi la race d’Israël cessera pour toujours d’être une nation devant moi.
37 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
Ainsi parle Yahweh: Si les cieux peuvent se mesurer en haut, et les fondements de la terre se sonder en bas, alors aussi je rejetterai toute la race d’Israël, à cause de tout ce qu’ils ont fait, — oracle de Yahweh.
38 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
Voici que des jours viennent, — oracle de Yahweh, où cette ville sera rebâtie pour Yahweh, depuis la tour de Hananéel jusqu’à la porte de l’Angle.
39 Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
Le cordeau à mesurer sera tiré en droite ligne sur la colline de Gareb, et il tournera vers Goa.
40 Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”
Et toute la vallée des cadavres et des cendres, et tous les champs jusqu’au torrent de Cédron, et jusqu’à l’angle de la porte des Chevaux, vers l’orient, seront des lieux saints à Yahweh, et ils ne seront jamais ni dévastés ni détruits.

< Irmiya 31 >