< Irmiya 26 >

1 A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
Na začetku kraljevanja Jojakíma, Jošíjevega sina, Judovega kralja, je prišla ta beseda od Gospoda, rekoč:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
»Tako govori Gospod: ›Stoj na dvoru Gospodove hiše in govori vsem Judovim mestom, ki pridejo oboževat v Gospodovo hišo, vse besede, ki sem ti jih zapovedal, da jim jih govoriš; ne zmanjšaj niti besede.
3 Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
Če bo tako, bodo prisluhnili in se obrnili, vsak človek iz svoje zle poti, da se lahko pokesam od zla, ki sem jim ga namenil storiti zaradi zla njihovih početij.
4 Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
Rekel jim boš: ›Tako govori Gospod: ›Če mi ne boste prisluhnili, da se ravnate po moji postavi, ki sem jo postavil pred vas,
5 in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
da prisluhnete besedam mojih služabnikov prerokov, ki sem jih pošiljal k vam; zgodaj sem jih vzdigoval in jih pošiljal, toda niste prisluhnili;
6 to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
potem bom to hišo naredil podobno Šilu in to mesto naredil prekletstvo vsem narodom zemlje.‹«
7 Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
Tako so duhovniki, preroki in vse ljudstvo slišali Jeremija govoriti te besede v Gospodovi hiši.
8 Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
Pripetilo se je torej, ko je Jeremija končal govorjenje vsega, kar mu je Gospod zapovedal, da govori vsemu ljudstvu, da so ga duhovniki in preroki in vse ljudstvo zgrabili, rekoč: »Zagotovo boš umrl.
9 Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
Zakaj si prerokoval v Gospodovem imenu, rekoč: ›Ta hiša bo podobna Šilu in to mesto bo zapuščeno, brez prebivalca?‹« In vse ljudstvo je bilo zbrano zoper Jeremija v Gospodovi hiši.
10 Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
Ko so Judovi princi slišali te stvari, potem so prišli gor iz kraljeve hiše h Gospodovi hiši in se usedli pri vhodu novih velikih vrat Gospodove hiše.
11 Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
Potem so duhovniki in preroki spregovorili princem in vsemu ljudstvu, rekoč: »Ta mož je vreden, da umre, kajti prerokoval je zoper to mesto, kakor ste slišali s svojimi ušesi.«
12 Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
Potem je Jeremija spregovoril vsem princem in vsemu ljudstvu, rekoč: » Gospod me je poslal, da prerokujem zoper to hišo in zoper to mesto vse besede, ki ste jih slišali.
13 Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
Zato sedaj poboljšajte svoje poti in svoja dejanja in ubogajte glas Gospoda, svojega Boga, in Gospod se bo pokesal od zla, ki ga je proglasil zoper vas.
14 Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
Poglejte, kar se mene tiče, jaz sem v vaši roki. Z menoj storite kakor se vam zdi dobro in primerno.
15 Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
Toda zagotovo vedite, da če me boste usmrtili, boste zagotovo privedli nedolžno kri nadse, nad to mesto in nad njegove prebivalce, kajti resnično me je k vam poslal Gospod, da v vaša ušesa govorim vse te besede.«
16 Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
Potem so princi in vse ljudstvo rekli duhovnikom in prerokom: »Ta mož ni vreden, da umre, kajti govoril nam je v imenu Gospoda, našega Boga.«
17 Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
Potem so vstali nekateri izmed starešin dežele in spregovorili vsemu zboru ljudstva, rekoč:
18 “Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
»Mihej Moréšečan je prerokoval v dneh Ezekíja, Judovega kralja in govoril vsemu Judovemu ljudstvu, rekoč: ›Tako govori Gospod nad bojevniki: ›Sion bo preoran kakor polje in Jeruzalem bo spremenjen v razvaline in gora hiše kakor visoki kraji gozda.
19 “Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
Ali ga je Judov kralj Ezekíja in ves Juda sploh dal usmrtiti? Mar se ni bal Gospoda in rotil Gospoda in se je Gospod pokesal zla, ki ga je proglasil zoper njih? Tako bi lahko prihranili veliko zlo zoper naše duše.
20 (To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
Tam pa je bil tudi človek, ki je prerokoval v Gospodovem imenu, Urijá, sin Šemajája iz Kirját Jearíma, ki je prerokoval zoper to mesto in zoper to deželo, glede na vse Jeremijeve besede.
21 Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
Ko je kralj Jojakím, z vsemi svojimi mogočnimi možmi in vsemi princi, slišal njegove besede, je kralj iskal, da ga usmrti. Toda ko je Urijá to slišal, je bil prestrašen in pobegnil ter odšel v Egipt.
22 Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
Kralj Jojakím pa je poslal može v Egipt, in sicer Ahbórjevega sina Elnatána in nekatere može z njim v Egipt.
23 Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
Ti so Urijá spravili iz Egipta in ga privedli h kralju Jojakímu, ki ga je usmrtil z mečem in njegovo truplo vrgel v grobove preprostega ljudstva.
24 Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.
Kljub temu je bila roka Šafánovega sina Ahikáma z Jeremijem, da ga ne bi predali v roko ljudstva, da ga usmrti.

< Irmiya 26 >