< Irmiya 26 >
1 A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
Au début du règne de Joïakim, fils de Josias, roi de Juda, la parole que voici arriva de la part de l’Eternel:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
Ainsi parle l’Eternel: "Tiens-toi dans la cour de la maison de l’Eternel, et adresse aux gens de toutes les villes de Juda qui sont venus se prosterner dans la maison de l’Eternel toutes les paroles que je t’ordonne de leur adresser; n’en retranche pas un mot.
3 Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
Peut-être écouteront-ils, se repentiront-ils chacun de leur mauvaise conduite et pourrai-je révoquer le malheur que je me propose de leur infliger à cause de la perversité de leurs actes.
4 Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
Tu leur diras donc: Ainsi parle l’Eternel: Si vous refusez de m’écouter, de suivre ma doctrine que j’ai promulguée devant vous,
5 in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
d’obéir aux paroles de mes serviteurs les prophètes que sans cesse et dès la première heure j’envoie vers vous, sans que vous leur prêtiez attention,
6 to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
je traiterai cette maison pareillement à silo, et de cette ville je ferai un objet de malédiction pour tous les peuples de la terre."
7 Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
Or, les prêtres, les prophètes et tout le peuple entendirent Jérémie prononcer ces paroles dans la maison de Dieu.
8 Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
Et quand Jérémie eut achevé de dire ce que l’Eternel lui avait ordonné de dire à tout le peuple, les prêtres, les prophètes et tout le peuple se saisirent de lui en s’écriant: "Il faut que tu meures!
9 Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
Pourquoi as-tu prophétisé au nom de l’Eternel en disant: Cette maison deviendra semblable à silo, et cette ville sera ruinée, privée d’habitants?" Tout le peuple s’attroupa autour de Jérémie dans la maison de Dieu.
10 Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
Lorsque les grands de Juda eurent connaissance de ces faits, ils se rendirent du palais du roi au Temple de l’Eternel et prirent place à l’entrée de la porte Neuve de l’Eternel.
11 Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
Alors les prêtres et les prophètes dirent aux grands et à tout le peuple: "Cet homme mérite la mort, car il a prophétisé contre cette ville, comme vous l’avez entendu de vos propres oreilles."
12 Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
Jérémie, s’adressant à tous les grands et au peuple entier, leur dit: "C’Est l’Eternel qui m’a envoyé pour prophétiser contre cette maison et contre cette ville toutes les paroles que vous avez entendues.
13 Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
Or, donc, améliorez votre conduite et vos oeuvres, écoutez la voix de l’Eternel, votre Dieu, pour que l’Eternel révoque le malheur qu’il a décrété contre vous.
14 Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
Quant à moi, je suis en votre pouvoir, traitez-moi comme il vous paraîtra bon et équitable.
15 Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
Toutefois, sachez bien que si vous me faites mourir, c’est du sang innocent que vous répandez sur vous, sur cette ville et ses habitants; car, en vérité, c’est l’Eternel qui m’a envoyé vers vous, pour faire entrer dans vos oreilles tous ces discours que je tiens."
16 Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
Alors les grands et tout le peuple dirent aux prêtres et aux prophètes: "Cet homme ne mérite pas la mort, car c’est au nom de l’Eternel, notre Dieu, qu’il nous a parlé."
17 Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
Puis, quelques-uns parmi les anciens du pays se levèrent et s’adressèrent en ces termes à toute l’assemblée du peuple:
18 “Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
"Michée, de Moréchet, prophétisait du temps d’Ezechias, roi de Juda, et voici ce qu’il disait à tout le peuple de Juda: Ainsi a parlé l’Eternel-Cébaoth: Sion sera labourée comme un champ, Jérusalem deviendra un monceau de ruines et la montagne du Temple une hauteur boisée.
19 “Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
Ezéchias, roi de Juda, et tout le peuple de Juda l’ont-ils condamné à mourir? N’A-t-on pas craint l’Eternel et cherché à apaiser sa colère? Aussi l’Eternel révoqua-t-il le mal qu’il avait décrété contre eux; et nous, nous chargerions nos âmes d’un si grand crime!"
20 (To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
Il y eut encore un homme qui prophétisait au nom de l’Eternel: c’était Ouria, fils de Chemaya, de Kiriat-Yearim. II prophétisait contre cette ville et contre ce pays exactement dans les mêmes termes que Jérémie.
21 Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
Le roi Joïakim eut connaissance de ses discours ainsi que tous ses hommes de guerre et tous les grands, et il chercha à le mettre à mort. Ouria en fut informé, il prit peur, s’enfuit et se rendit en Egypte.
22 Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
Alors le roi Joïakim envoya des gens en Egypte: c’était Elnathan, fils d’Akhbor, et quelques autres avec lui pour l’accompagner en Egypte.
23 Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
Ils firent sortir Ouria hors d’Egypte et l’amenèrent au roi Joïakim, qui le fit périr par le glaive et ordonna de jeter son cadavre parmi les tombes du bas peuple.
24 Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.
Toutefois, Ahi’kam, fils de Chafan, protégea Jérémie et empêcha qu’il ne fût livré au pouvoir du peuple et mis à mort.