< Irmiya 23 >

1 “Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
“Woe to shepherds destroying, And scattering the flock of My pasture,” A declaration of YHWH.
2 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
Therefore, thus said YHWH, God of Israel, Against the shepherds who feed My people: “You have scattered My flock, and drive them away, And have not inspected them, Behold, I am charging on you the evil of your doings,” A declaration of YHWH.
3 “Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
“And I gather the remnant of My flock Out of all the lands to where I drove them, And have brought them back to their fold, And they have been fruitful, and multiplied.
4 Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
And I have raised shepherds for them, And they have fed them, And they no longer fear, nor are frightened, Nor are they lacking,” A declaration of YHWH.
5 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
“Behold, days are coming,” A declaration of YHWH, “And I have raised a righteous shoot to David, And a king has reigned and acted wisely, And done judgment and righteousness in the earth.
6 A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
Judah is saved in His days, and Israel dwells confidently, And this [is] His Name that YHWH proclaims Him: Our Righteousness.
7 “Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
Therefore, behold, days are coming,” A declaration of YHWH, “And they no longer say, YHWH lives who brought up The sons of Israel out of the land of Egypt,
8 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
But—YHWH lives, who brought up, And who brought in, the seed of the house of Israel, From the land of the north, And from all the lands to where I drove them, And they have dwelt on their own ground!”
9 Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
In reference to the prophets: My heart has been broken in my midst, All my bones have fluttered, I have been as a man—a drunkard, And as a man—wine has passed over him, Because of YHWH, and of His holy words.
10 Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
For the land has been full of adulterers, For the land has mourned because of these, The pleasant places of the wilderness have dried up, And their course is evil, and their might—not right.
11 “Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
“For both prophet and priest have been profane, Indeed, I found their wickedness in My house,” A declaration of YHWH.
12 “Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
“Therefore their way is as slippery places to them, They are driven into thick darkness, And they have fallen in it, For I bring in calamity against them, The year of their inspection,” A declaration of YHWH.
13 “A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
“And I have seen folly in prophets of Samaria, They have prophesied by Ba‘al, And cause My people—Israel—to err.
14 A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
And I have seen a horrible thing in prophets of Jerusalem, Committing adultery, and walking falsely, Indeed, they strengthened the hands of evildoers, So that they have not turned back, Each from his wickedness, All of them have been as Sodom to me, And its inhabitants as Gomorrah.”
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
Therefore, thus said YHWH of Hosts, concerning the prophets: “Behold, I am causing them to eat wormwood, And have caused them to drink water of gall, For from prophets of Jerusalem Profanity has gone forth to all the land.”
16 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
Thus said YHWH of Hosts: “You do not listen to the words Of the prophets who are prophesying to you, They are making you vain things, They speak a vision of their own heart, Not from the mouth of YHWH.
17 Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
Diligently saying to those despising, The word of YHWH: Peace is for you, And [to] everyone walking in the stubbornness of his heart, they have said: Evil does not come to you.”
18 Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
For who has stood in the counsel of YHWH, And sees and hears His word? Who has regarded My word, and listens?
19 Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
Behold, a whirlwind of YHWH—Fury has gone out, even a piercing whirlwind, It stays on the head of the wicked.
20 Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
The anger of YHWH does not turn back Until His doing, and until His establishing, The thoughts of His heart, In the latter end of the days You attend to it with understanding.
21 Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
“I have not sent the prophets, and they have run, I have not spoken to them, and they have prophesied.
22 Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
But if they stood in My counsel, Then they cause My people to hear My words, And they turn them back from their evil way, And from the evil of their doings.
23 “Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
[Am] I a God near,” A declaration of YHWH, “And not a God far off?
24 Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
Is anyone hidden in secret places, And I do not see him?” A declaration of YHWH, “Do I not fill the heavens and the earth?” A declaration of YHWH.
25 “Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
“I have heard that which the prophets said, Who prophesy falsehood in My Name, saying, I have dreamed, I have dreamed.
26 Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
Until when is it in the heart of the prophets? The prophets of falsehood, Indeed, prophets of the deceit of their heart,
27 Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
Who are devising to cause My people To forget My Name by their dreams, That they each recount to his neighbor, As their fathers forgot My Name for Ba‘al.
28 Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
The prophet with whom [is] a dream, Let him recount the dream, And he with whom [is] My word, Let him truly speak My word. What does the straw [have to do] with the grain?” A declaration of YHWH.
29 “Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
“Is it not thus? My word [is] as fire,” A declaration of YHWH. “And as a hammer—it breaks a rock in pieces.
30 “Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
Therefore, behold, I [am] against the prophets,” A declaration of YHWH, “Each stealing My words from his neighbor.
31 I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
Behold, I [am] against the prophets,” A declaration of YHWH, “Who are making their tongue smooth, And they affirm—an affirmation.
32 Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
Behold, I [am] against the prophets of false dreams,” A declaration of YHWH, “And they recount them, and cause My people to err, By their falsehoods, and by their instability, And I have not sent them, Nor have I commanded them, And they are not profitable to this people at all,” A declaration of YHWH.
33 “Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
“And when this people, or the prophet, Or a priest, asks you, saying, What [is] the burden of YHWH? Then you have said to them: You [are] the burden, and I have left you,” A declaration of YHWH.
34 In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
“And the prophet, and the priest, and the people, That says, The burden of YHWH, I have seen after that man, and after his house.
35 Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Thus you each say to his neighbor, And each to his brother: What has YHWH answered? And what has YHWH spoken?
36 Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
And you do not mention the burden of YHWH anymore, For the burden to each is His word, And you have overturned the words of the living God, YHWH of Hosts, our God.
37 Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Thus you say to the prophet, What has YHWH answered you? And what has YHWH spoken?
38 Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
And if you say, The burden of YHWH, Therefore, thus said YHWH: Because of your saying this word, The burden of YHWH, And I send to you, saying, You do not say, The burden of YHWH.
39 Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
Therefore, behold, I have utterly taken you away, And I have sent you out, And the city that I gave to you, And to your fathers, from before My face,
40 Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”
And I have put continuous reproach on you, And continuous shame that is not forgotten!”

< Irmiya 23 >