< Irmiya 18 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
RAB Yeremya'ya şöyle seslendi:
2 “Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
“Kalk, çömlekçinin işliğine git; orada sana sesleneceğim.”
3 Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
Bunun üzerine çömlekçinin işliğine gittim. Çark üzerinde çalışıyordu.
4 Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
Yaptığı balçıktan kap elinde bozulunca çömlekçi balçığa istediği biçimi vererek başka bir kap yaptı.
5 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana yine seslendi:
6 “Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
“Bu çömlekçinin yaptığını ben de size yapamaz mıyım, ey İsrail halkı? diyor RAB. Çömlekçinin elinde balçık neyse, siz de benim elimde öylesiniz, ey İsrail halkı!
7 A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
Bir ulusun ya da krallığın kökünden söküleceğini, yıkılıp yok edileceğini duyururum da,
8 in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
uyardığım ulus kötülüğünden dönerse, başına felaket getirme kararımdan vazgeçerim.
9 In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
Öte yandan, bir ulusun ya da krallığın kurulup dikileceğini duyururum da,
10 in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
o ulus sözümü dinlemeyip gözümde kötü olanı yaparsa, ona söz verdiğim iyiliği yapmaktan vazgeçerim.
11 “Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
“Bu nedenle Yahuda halkıyla Yeruşalim'de yaşayanlara de ki, ‘RAB şöyle diyor: İşte size bir felaket tasarlıyor, size karşı bir düzen kuruyorum. Onun için her biriniz kötü yolundan dönsün, yaşantınızı da davranışlarınızı da düzeltin.’
12 Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
Ama onlar, ‘Boş ver! Biz kendi tasarılarımızı sürdüreceğiz; her birimiz kötü yüreğinin inadı uyarınca davranacak’ diyecekler.”
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
Bu yüzden RAB diyor ki, “Uluslar arasında soruşturun: Böylesini kim duydu? Erden kız İsrail Çok korkunç bir şey yaptı.
14 Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
Kayalık bayırlardan Lübnan'ın karı hiç eksik olur mu? Uzaktan akan soğuk sular hiç kesilir mi?
15 Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
Oysa halkım beni unuttu, Değersiz ilahlara buhur yaktı. Bu ilahlar gidecekleri yollarda, Eski yollarda sendelemelerine neden oldu; Onları sapa, bitmemiş yollarda yürüttü.
16 Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
Ülkeleri viran edilecek, Sürekli alay konusu olacak; Oradan her geçen şaşkın şaşkın Başını sallayacak.
17 Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
Onları düşmanlarının önünde Doğu rüzgarı gibi dağıtacağım; Yıkım günü yüzümü değil, Sırtımı çevireceğim onlara.”
18 Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
Bunun üzerine, “Haydi, Yeremya'ya karşı bir düzen kuralım!” dediler, “Çünkü yasayı öğretecek kâhin, öğüt verecek bilge, Tanrı sözünü bildirecek peygamber hiç eksik olmayacak. Gelin, ona sözle saldıralım, söylediklerini de dinlemeyelim.”
19 Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
Dinle beni, ya RAB, Beni suçlayanların dediklerini işit!
20 Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
İyiliğe karşı kötülük mü yapmalı? Ama onlar bana çukur kazdılar. Onlara duyduğun öfkeyi yatıştırmak, Onların iyiliğini dilemek için Senin önünde nasıl durduğumu anımsa.
21 Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
Bu yüzden çocuklarını kıtlığa ver, Kılıcın ağzına at. Karıları çocuksuz, dul kalsın, Erkeklerini ölüm alıp götürsün, Gençleri savaşta kılıçtan geçirilsin.
22 Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
Sen üzerlerine ansızın akıncılar gönderdiğinde, Evlerinden çığlıklar duyulsun. Çünkü beni yakalamak için çukur kazdılar, Ayaklarıma gizli tuzak kurdular.
23 Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.
Beni öldürmek için kurdukları düzenlerin hepsini Biliyorsun, ya RAB. Bağışlama suçlarını, Günahlarını önünden silme. Yığılıp kalsınlar senin önünde. Öfkeliyken uğraş onlarla.

< Irmiya 18 >