< Irmiya 16 >
1 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Jehovah came to me, saying:
2 “Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
Take thee not a wife; Have no sons or daughters in this place!
3 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
For thus saith Jehovah concerning the sons and the daughters That are born in this place, And concerning their mothers that bore them, And concerning their fathers that begat them in this land;
4 “Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
By deadly diseases shall they die; They shall not be lamented nor buried; They shall become dung upon the face of the earth; By the sword also and by famine shall they be consumed, And their carcasses shall be food for the birds of heaven And the beasts of the earth.
5 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
For thus saith Jehovah: Enter not into the house of wailing; Go not to lament; Comfort them not! For I have taken away my peace from this people, saith Jehovah, My kindness and mercy.
6 “Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
The great and the small in this land shall die; They shall not be buried nor lamented; No one shall cut himself for them, Nor shall any one make himself bald for them.
7 Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
Men shall not break bread for them in their grief, To comfort them for the dead, Nor give them the cup of consolation to drink, On account of a lost father or mother.
8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
Neither enter thou into the house of feasting, To sit down with them to eat and to drink!
9 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
For thus saith Jehovah of hosts, the God of Israel: Behold, I am about to cause to cease from this place, Before your eyes, in your days, The voice of joy and the voice of mirth, The voice of the bridegroom and the voice of the bride.
10 “Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
And when thou shalt have declared to this people all these things, and they shall say to thee, “Why hath Jehovah pronounced against us all this great evil? What is our iniquity, and what our sin, which we have committed against Jehovah our God?”
11 Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
Then shalt thou say to them: Because your fathers have forsaken me, saith Jehovah, And have walked after strange gods, And have served them and worshipped them, And have forsaken me, and not kept my law.
12 Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
And ye yourselves have done worse than your fathers; For, behold, ye walk every one after the perverseness of his evil heart, And do not hearken to me.
13 Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
Therefore will I cast you forth from this land Into a land unknown to you and to your fathers; And there shall ye serve strange gods day and night; For I will show you no favor.
14 “Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
Yet behold the days shall come, saith Jehovah, When men shall no more say, “As Jehovah liveth Who brought up the children of Israel from the land of Egypt,”
15 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
But, “As Jehovah liveth Who brought up the children of Israel from the land of the North, And from all the lands whither he had driven them.” For I will bring them again into their own land, Which I gave to their fathers.
16 “Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
Behold, I will send many fishers, saith Jehovah, who shall fish them, And then will I send many hunters who shall hunt them From every mountain, and from every hill, and from the holes of the rocks.
17 Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
For mine eyes are upon all their ways; They are not concealed from my view, Nor is their iniquity hidden from mine eyes.
18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
And I will requite their former and their repeated iniquities and sins, Because they have polluted my land with carcasses offered to their idols, And filled my inheritance with their abominable things.
19 Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
O Jehovah, my strength and my fortress, My refuge in the day of distress! To thee shall the nations come from the ends of the earth, And shall say, “Truly our fathers inherited delusion, Vain and unprofitable things.
20 Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
Shall one make for himself gods Which are no gods?”
21 “Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.
Therefore, behold, I will this time cause them to feel, I will cause them to feel my hand and my might, And they shall know that my name is Jehovah.