< Irmiya 15 >

1 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, zuciyata ba za tă komo ga mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana! Su tafi!
And YHWH says to me: “Though Moses and Samuel should stand before Me, My soul is not toward this people, Send from before My face, and they go out.
2 In kuma suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Waɗanda aka ƙaddara ga mutuwa, ga mutuwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga takobi, ga takobi za su; waɗanda aka ƙaddara ga yunwa, ga yunwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga zaman bauta, ga zaman bauta za su.’
And it has come to pass, when they say to you, To where do we go out? That you have said to them, Thus said YHWH: Those who [are] for death—to death, And those who are for the sword—to the sword, And those who are for famine—to famine, And those who are for captivity—to captivity.
3 “Zan aika musu da iri masu hallakarwa guda huɗu,” in ji Ubangiji, “takobi zai kashe, karnuka za su kwashe, tsuntsaye da namun jeji kuma su cinye su kuma hallaka.
And I have appointed four kinds over them,” A declaration of YHWH, “The sword to slay, and the dogs to drag, And the bird of the heavens, And the beast of the earth, to consume and to devour.
4 Zan sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manasse ɗan Hezekiya sarkin Yahuda ya aikata a Urushalima.
And I have given them for a trembling To all kingdoms of the earth, Because of Manasseh son of Hezekiah king of Judah, For that which he did in Jerusalem.
5 “Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi makoki dominki? Wa zai dakata ya tambayi lafiyarki?
For who has pity on you, O Jerusalem? And who bemoans for you? And who turns aside to ask of your welfare?
6 Kin ƙi ni,” in ji Ubangiji. “Ki ci gaba da ja da baya. Ta haka zan ɗibiya hannuwana a kanki in hallaka ki; ba zan ƙara nuna miki jinƙai ba.
You have left Me,” A declaration of YHWH, “You go backward, And I stretch out My hand against you, And I destroy you, I have been weary of relenting,
7 Zan sheƙe ki da abin sheƙewa a ƙofofin birnin ƙasar. Zan kawo baƙin ciki da hallaka a kan mutanena, gama ba su canja hanyoyinsu ba.
And I scatter them with a fan, In the gates of the land, I have bereaved [them], I have destroyed My people, They did not turn back from their ways.
8 Zan ƙara yawan gwaurayensu su fi yashin teku yawa. Da tsakar rana zan kawo mai hallakarwa a kan iyaye mata na samarinsu; farat ɗaya zan kawo musu wahala da razana.
Its widows have been more to Me than the sand of the seas, I brought on them—against the mother—A young man—a spoiler—at noon. I caused wrath and trouble to fall on her suddenly.
9 Mahaifiya’ya’ya bakwai za tă suma ta ja numfashinta na ƙarshe. Ranarta zai fāɗi tun lokacin bai yi ba; za tă sha kunya a kuma wulaƙanta ta. Zan sa a kashe raguwa da takobi a gaban abokan gābansu,” in ji Ubangiji.
The bearer of seven has languished, She has breathed out her spirit, Her sun has gone in while yet day, It has been ashamed and confounded, And I give up their remnant to the sword before their enemies,” A declaration of YHWH.
10 Kaitona, mahaifiyata, da kika haife ni, mutumin da dukan ƙasa take faɗa take kuma gardama da shi! Ban ba da bashi ko in ci bashi ba, duk da haka kowa yana zagina.
Woe to me, my mother, For you have borne me, A man of strife and a man of contention to all the land, I have not lent on usury, Nor have they lent on usury to me—All of them are reviling me.
11 Ubangiji ya ce, “Tabbatacce zan cece ka don alheri; tabbatacce zan sa abokan gābanka su yi roƙo gare ka a lokacin masifa da kuma lokacin wahala.
YHWH said, “Did I not direct you for good? Did I not intercede for you in a time of evil, And in a time of adversity, with the enemy?
12 “Mutum zai iya karye ƙarfe ƙarfe daga arewa, ko tagulla?
Does one break iron, Northern iron and bronze?
13 “Dukiyarku da arzikinku zan ba da su ganima, babu tara, saboda duka zunubanku ko’ina a ƙasar.
I give your strength and your treasures for a prey—not for price, Even for all your sins, and in all your borders.
14 Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina zai yi ƙuna kamar wuta da za tă yi ƙuna a kanku.”
And I have caused your enemies To pass over into the land [that] You have not known, For a fire has been kindled in My anger, It burns against you.”
15 Ka gane, ya Ubangiji; ka tuna da ni ka kuma lura da ni. Ka yi mini ramuwa a kan masu tsananta mini. Cikin jimirinka, kada ka ɗauke ni; ka tuna yadda na sha zagi saboda kai.
You, You have known, O YHWH, Remember me, and inspect me, And take vengeance for me of my pursuers, In Your long-suffering do not take me away, Know [that] I have borne reproach for You.
16 Sa’ad da maganganunka suka zo, na cinye su; suka zama abin farin ciki zuciyata kuma ta yi murna, gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Your words have been found, and I eat them, And Your word is to me for a joy, And for the rejoicing of my heart, For Your Name is called on me, O YHWH, God of Hosts.
17 Ban taɓa zauna a cikin’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
I have not sat in an assembly of deriders, Nor do I exult, because of your hand—I have sat alone, For You have filled me [with] indignation.
18 Me ya sa wahalata ba ta ƙarewa mikina kuma ba ya warkuwa? Za ka zama mini kamar rafi mai yaudara ne, kamar maɓulɓulan da ta kafe ne?
Why has my pain been continuous? And my wound incurable? It has refused to be healed, You are surely as a failing stream to me, Waters [that are] not steadfast.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “In ka tuba, zan maido da kai don ka bauta mini; in ka ambaci maganganu masu kyau, ba marasa kyau ba, za ka zama kakakina. Bari wannan mutane su juyo gare ka, amma kada ka juye gare su.
Therefore, thus said YHWH: “If you turn back, then I bring you back, You stand before Me, And if you bring out the precious from the vile, You are as My mouth! They return to you, And you do not return to them.
20 Zan mai da kai katanga ga wannan mutane, katanga mai ƙarfi na tagulla; za su yi yaƙi da kai amma ba za su yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in kuɓutar in kuma cece ka,” in ji Ubangiji.
And I have made you to this people For a wall—bronze—fortified, And they have fought against you, And they do not prevail against you, For I [am] with you to save you, And to deliver you,” A declaration of YHWH,
21 “Zan cece ka daga hannuwan mugaye in ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”
“And I have delivered you from the hand of evildoers, And I have ransomed you From the hand of the terrible!”

< Irmiya 15 >